Ganduje Ya Ba Da Kyautar Gida Da Miliyan N3 Ga Yar Kano Da Ta Zo Ta Biyu a Gasar Karatun Al-Qur’ani Na Duniya

Ganduje Ya Ba Da Kyautar Gida Da Miliyan N3 Ga Yar Kano Da Ta Zo Ta Biyu a Gasar Karatun Al-Qur’ani Na Duniya

  • Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya yi wa yar jihar da ta zo ta biyu a gasar Al-Qur'ani na duniya sha tara ta arziki
  • Ganduje ya ba wa Aisha Abubakar Dorayi kyautar gida da tsabar kudi har naira miliyan 3
  • A cewarsa an yi hakan ne domin karfafawa sauran al'ummar jihar gwiwa tare da zaburar da su

Kano - Gwamnatin Jihar Kano ta yi alkawarin bayar da sabon kerarren gida da naira miliyan 3 ga yar asalin jihar, Aisha Abubakar Dorayi, saboda zuwa ta biyu da ta yi a gasar karatun Al-Qur'ani na duniya, wanda aka yi a kasar Dubai.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi alkawarin ne yayin taron majalisar zartarwa na jihar wanda ya gudana a gidan gwamnatin Kano, Daily Trust ta rahoto.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Buhari Zai Shilla Ingila Don Halartar Nadin Sarautar Sarki Charles

Gwamna Abdullahi Ganduje
Ganduje Ya Ba Da Kyautar Gida Da Miliyan N3 Ga Yar Kano Da Ta Zo Ta Biyu a Gasar Karatun Al-Qur’ani Na Duniya Hoto: The Guardian
Source: UGC

Dalilin da yasa muka yi wa yarinyar kyauta, Ganduje

Ya ce an yanke shawarar bata kyautar ne domin karfafawa sauran yan jihar gwiwar jajircewa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ganduje ya ce:

"Wannan nasarar ba na Aisha bace ita kadai, ba na iyayenta bane su kadai, na jihar Kano ne. Wannan ne dalilin da yasa muka yanke shawarar zaburar da ita da kyautar gida a cikin sabbin gidajen da aka ginawa malamai a jihar. Mun kuma yanke shawarar ba yarinyar tsabar kudi naira miliyan 3. Muna alfahari da ita."

Da yake jawabi bayan sanarwar, wacce aka karrama, Aisha Abubakar Dorayi daga karamar hukumar Gwale ta jihar ta yaba da wannan karamci da aka yi mata sannan ta yi alkawarin ci gaba da zage damtse.

Ta yabawa iyayenta, malamai da abokan karatunta da ke karkafa mata gwiwa wajen samun ilimi har zuwa wannan matakin.

Kara karanta wannan

Kwamishinan Zaben Adamawa: Ban Yi Nadamar Ayyana Binani a Matsayin Gwamna Ba

Ta ce:

"Ina farin ciki a yau da gwamnatin jihar ta lura da wannan nasarar. Amma nasarar namu ne mu dukka, musamman malamai da iyayena. Sun tsaya ka'in da na'in tare da ni don cimma wannan a yau. Ba zan iya gode masu ba. Allah ya saka masu da alkhairi dukka."

Bidiyon mahaukaci da ke tsafiya mai nisa don daukar daraji a jami'ar Benin ya dauka hankali

A wani labarin, wani matashi mai lalurar tabin hankali ya ja hankalin mutane da dama a soshiyal midiya bayan cin karo da bidiyonsa zaune a cikin jami'ar Benin.

A tunaninsa, matashin ya ce yana zuwa daukar darasi ne domin dai a kan gano shi zaune da takarda da biro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: