Gwamna Sanwo-Olu Ya Saki Hotunan Motocin Bas Masu Amfani Da Lantarki Na Farko a Lagas
- Gwamna Babajide Sanwo-Olu zai gwangwaje al'ummar Lagas da wani sabon yunkuri da ya yi a bangaren sufuri a jihar
- Gwamnatin jihar Lagas ta sanar a shafinta na Twitter cewa ta karbi rukunin farko na motocin bas masu amfani da lantarki
- Sabbin motocin bas din suna iya tafiya mai tsawon kilomita 280 idan suka samu cikakken chaji
Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya sanar da isowar rukunin farko na motocin bas masu amfani da lantarki da za su dunga jigilar jama'a a jihar Lagas.
Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana cewa ci gaban yana daga cikin kokarin gwamnatinsa na kara zamanantar da kowane bangare na Lagas.

Asali: Twitter
Ya ce sabbin bas din masu amfani da lantarkin za su rage gurbatattun hayaki da kuma karfafa aiki a bangaren sufuri.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya fada ma mazauna Lagas da su tsammaci tsarin sufurin gwamnati mai tsafta.

Kara karanta wannan
Binani ce ta ci zabe: Hudu Ari ya fasa kwai, ya ce manya a INEC sun karbi cin hanci daga Fintiri
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jama'a sun yi martani a kan sabbin motocin bas masu amfani da lantarki a Lagas
Bayan gwamnan ya wallafa labarin a soshiyal midiya, jama'a sun jinjina masa. Sai dai wasu sun soki hakan.
Mgbojikwe Peter Obi Yusuf Datti @cuppydat ya ce:
"Motar bas da zai tsaya a tsakiyar ekoncos ba Nepa da za a yi chajinsa."
Kevin Doge @ogbodo_kevin sya ce:
"Motar da za a dade ana kula da shi baya Najeriya."
Daniel Ayeni @danizydonn ya yi martani:
"Ci gaba mai kyau. Menene cikkken tasarin amfaninsa a wajen jama'a? Ina jira na ga tasirin da bas dinnan da jiragen kasa za su yi wajen al'umma a Lagas."
Matan da aka dauka aikin sharar titi kan albashi N8000 sun magantu
A wani labarin, wasu mata da mazajensu suka mutu wadanda aka dauka aikin sharar titi domin rage masu radadi a jihar Filato sun bayyana irin gwagwarmayar da suke sha a kan albashin N8000.
Matan sun bayyana cewar suna shan wahala saboda har yanzu gwamnati bata yi masu karin albashi ba sannan kuma wasu watannin ma ba a biyansu albashi, ga shi abun da suke samu baya isan su daukar dawainiyar kansu da na iyalin su.
Asali: Legit.ng