An Yi Bata Kash Da ’Yan Bindiga a Kaduna, an Hallaka ’Yan Bindiga Hudu

An Yi Bata Kash Da ’Yan Bindiga a Kaduna, an Hallaka ’Yan Bindiga Hudu

  • Rundunar sojin Najeriya ta yi nasarar hallaka wasu 'yan ta'addan da suka kai hare-hare wasu yankunan jihar Kaduna
  • An hallaka 'yan bindiga hudu, an kwato makamai da kudade daga hannun 'yan bindigan da aka hallaka
  • Rundunar sojin Najeriya na ci gaba da samun nasara kan 'yan bindiga a yankuna daban-daban na kasar nan

Jihar Kaduna - Rundunar Operation Forest Sanity ta hallaka wasu ‘yan ta’adda hudu tare da kwato makamai da wasu kayayyakin aikata kaifi a jihar Kaduna.

Wannan na fitowa ne daga bakin Manjo Janar Musa Danmadami, daraktan yada labarai na gidan soja a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Abuja, PM News ta ruwaito.

Danmadami ya bayyana cewa, jami’an tsaron sun dakile harin ‘yan bindiga a yankin Rafin Sarki a karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna a ranakun Lahadi da Litinin.

Kara karanta wannan

Shikenan: Daga karshe, an kashe shugaban 'yan bindigan da ya addabi mazauna jiharsu Buhari

'Yan bindiga hudu aka kashe a jihar Kaduna a makon nan
An Yi Bata Kash Da ’Yan Bindiga a Kaduna, an Hallaka ’Yan Bindiga Hudu | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Yadda aka hallaka 'yan bindigan tare da kwto makamai

Ya kuma kara da cewa, an fatattakin ‘yan bindiga tare da kashe biyu da kuma kwato makami AK-47.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya kara da cewa, rundunar a ranar Talata ta yi kwanton bauna ga ‘yan bindiga kan wasu ‘yan bindiga a kauyen Rafin Taba, inda aka kashe ‘yan ta’adda biyu.

Ya ce jami’ai sun kwato bindigogi AK-47, alburusai, wayoyin hannu, adda, babura guda biyu da kudi N206,000.

Sanarwar ta ce:

"Babban ofishin rundunar sojoji ta yabawa dakarun Operation Forest Sanity kuma tana karfafawa jama'a gwiwa da su ba sojoji sahihan bayanan ‘yan ta’adda masu aikata laifuka.”

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.