Bankunan Najeriya Na Fama da Karancin Sabbin Kudade a Najeriya, Bankuna Da ’Yan Kasa Sun Koka

Bankunan Najeriya Na Fama da Karancin Sabbin Kudade a Najeriya, Bankuna Da ’Yan Kasa Sun Koka

  • Sabbin kudaden da gwamnatin Najeriya ta kaddamar makwannin baya tuni suka fara yawo a hukumance a ranar Alhamis 15 ga watan Disamba
  • Kwastomomi da yawa a bankunan Najeriya sun bayyana damuwar rashin samun sabbin kudaden a bankunan kasar nan
  • Bankunan Najeriya sun koka da cewa, basu samu adadi isasshe na sabbin kudaden daga Babban Bankin Kasa ba (CBN)

A ranar Alhamis 15 ga watan Disamba ne a hukumance aka fara kashe sabbin kudaden da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sanar da sake wa fasali a watan jiya.

‘Yan Najeriya sun yi tururuwa zuwa banki, amma suka samu matsalar rashin samun adadin da suke bukata na sabbin kudaden saboda bankunan da kansu basu sami kudaden da yawa ba.

‘Yan Najeriya sun koka, sun kuma yi martani mai zafi game da rashin samun sabbin kudaden a lokacin da suka nema a bankunan kasar nan.

Kara karanta wannan

Borno: An kassara Boko Haram, sojin sama sun kashe manyan mayakan da ake ji dasu

'Yan Najeriya sun je neman sabon kudi banki, basu sami komai ba
Bankunan Najeriya Na Fama da Karancin Sabbin Kudade a Najeriya, Bankuna Da ’Yan Kasa Sun Koka | Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

A nasu bangaren, bankuna a Najeriya sun yi bayani, sun ce basu samu adadin kudaden masu yawa bane daga CBN.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Batun sauya fasalin Naira

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ya ambata a ranar 26 ga watan Oktoba cewa, CBN zai sake fasalin Naira; N200, N500 da N1,000, inda yace tsoffin wadannan kudade kuwa za su daina amfani a watan Janairun badi.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, gwamnan na CBN ya ce, bankin zai yi aiki tukuru wajen tabbatar da rage yawan kudade a hannun jama’a domin magance matsalolin hauhawar farashi, rashin tsaro da yaduwar kudin bogi.

Kwastomomi sun fara kokawa game da rashin sabbin kudade a banki

A jihar Legas, wasu kwastomomi sun ziyarci bankuna da dama, sun kuma bayyana kokensu game da rashin sabbin kudin a kanta.

Da yawan bakunan sukan ce ko dai babu kudaden a kasa, ko kuma sun riga sun rabarwa jama’a.

Kara karanta wannan

Tashin hankali yayin da motoci biyu suka yi karo, mutum 1 ya hallaka, yawa sun jikkata

Wasu bankunan kuwa, sun ce basu samu damar karbar sabbin kudaden daga CBN ba kwata-kwata.

Hakazalika, injunan cire kudi na ATM na ci gaba da bayar tsoffin kudade kamar dai yadda aka saba a baya.

Babu sabbin kudade a wasu bankunan Gombe

Da sanyin safiyar ranar Juma’a, wakilin Legit.ng Hausa a jihar Gombe ya ziyarci daya daga cikin bakunan da ke Commercial Area a jihar, inda ya gwada cire kudi, tabbas tsoffin takardun Naira bankunan ke bayarwa.

Hakazalika, masu sana’ar cire kudi ta POS suna ci gaba da ba da tsoffin kudade ne tare da bayyana cewa, basu samu damar ganin alamar sabbin Naira ba.

A wani bangaren kuma, ya ziyarci wani bankin kasuwanci, nan ma bai samu sabbin kudaden da aka kaddamar ba.

Ma'ikacin banki ya ce bai ga lamar sabbin kudade a bankinsu ba, don haka basu ba wani kwastoma ba.

Wani kwastoman da yazo cire kudi, Muhammad Sa’idu ya shaida cewa:

Kara karanta wannan

Kila CBN Ya Canza Shawara, Sanatoci Sun Ce a Ajiye Batun Canjin Kudi Sai Yunin 2023

“Ban san ko a wasu bankuna ba, amma anan dai kam babu alamar sabbin kudi. Ina da aboki mai aiki a nan, ya ce ba a kawo musu sabbin kudi ba.
“Watakila ko Abuja da Legas, tunda a irin can ne komai ke fara tabbata kafin jihohinmu Arewa maso Gabas.”

A wani bankin kuma,Yahya Isa Khalifa cewa ya yi:

“A hoto muke gani, ni dama samun sabbin kudin nan bai dame ni ba. Na saba da amfani da waya ta. Kuma mutane mun cika gaggawa, kwana nawa ne za mu samu sabbin kudin har sai mun gaji?”

Wata mata kuwa, ta koyawa duniya yadda ake ajiyar kudi cikin sauki ba tare da wata matsala ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.