Sabon Gwamnan Jihar Ekiti Ya Yi Muhimman Nade-Nade Biyu Na Farko, Ya Kulle Asusu

Sabon Gwamnan Jihar Ekiti Ya Yi Muhimman Nade-Nade Biyu Na Farko, Ya Kulle Asusu

  • Gwamanan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya naɗa mutum biyu karon farko bayan shiga Ofis a matsayin sabon gwamna ranar Lahadi
  • Gwamnan ya naɗa Mace kuma Musulma, Habibat Adubairo, a matsayin sakatariyar gwamnatinsa
  • Ya kuma naɗa Sakataren watsa labarai sannan ya ba da umarnin kulle dukkanin asusun gwmanatin Ekiti

Ekiti - Sabon gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya naɗa Dakta Habibat Adubiaro, a matsayin Sakatariyar gwamnatin jiha, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Gwamna Oyebanji ya kuma amince da naɗin Mista Yinka Oyebode, a matsayin Sakataren watsa labarai (CPS).

Gwamna Biodun Oyebanji, na jihar Ekiti.
Sabon Gwamnan Jihar Ekiti Ya Yi Muhimman Nade-Nade Biyu Na Farko, Ya Kulle Asusu Hoto: Biodun Oyebanji.
Asali: Facebook

Wannan na kunshe a wasu sanarwa guda biyu daban-daban masu ɗauke da sa hannun shugaban ma'aikata, Mista Bamidele Agbede, ranar Lahadi jim kaɗan bayan rantsar da shi.

Naɗin guda biyu, a cewar sabon gwamnan da ya kama aiki ranar 16 ga watan Oktoba, 2022, zasu fara aiki ne nan take ba da ɓata lokaci ba.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: An Rantsar da Sabon Gwamnan APC Tare da Mataimakiyarsa, Hotuna Sun Fito

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Habibat Adubiaro, cikakkiyar Musulma, ta yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta musamman a zangon farko na mulkin tsohon gwamna Ayodele Fayose.

A halin yanzun ita ce shugabar ƙungiyar mata musulmai ta ƙasa reshen jihar Ekiti, 'Federation of Muslim Women’s Association of Nigeria.'

A ɗaya bangaren kuma, Mista Oyebode ɗan asalin garin Ido Ile, ƙaramar hukkumar Ekiti ta yamma, a zangon mulkin farko na gwamna Fayemi aka naɗa shi babban mai taimaka wa kan harkokin yaɗa labarai daga bisani aka mai da shi CPS.

Fayemi ya sake naɗa Oyebode a wannan muƙami bayan ya dawo zango na biyu a 2018 kuma ya yi aiki har zuwa ranar karshe gabanin gwamna Oyebanji ya sabunta naɗa shi a muƙamin.

Sabon Gwamnan ya rufe Asusun gwamnati

Bayan naɗe-naɗen kuma, gwamna Oyebanji, ya ba da umarnin garkame dukkanin asusun gwamnati har sai baba ta gani.

Kara karanta wannan

An Samu Sabon Cigaba da Rikicin Atiku da Gwamna Wike, Jam'iyyar PDP Ta Ɗage Yakin Neman Zaɓe

A wata sanarwa da sakataren watsa labarai, Yinka Oyebode, ya fitar, gwamnan ya umarci kowane Akanta ya bi wannan umarnin nan take.

A wani labarin kuma Manyan Alkawurra Uku da Atiku Ya Daukar Wa Jagororin Arewa a Kaduna

Atiku Abubakar ya yi alkawarin magance matsalar tsaro da ya addabi yankin arewa idan ya ɗare shugaban kasa a 2023.

Ɗan takarar kujera lamba ɗaya a inuwar PDP yace ya shirya tsaf wajen tsamo tattalin arzikin kasar nan daga durkushe wa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel