Gwamnatin Katsina Ta Ware N1.5bn Domin Kawo Karshen Matsalar Rashin Tsaro

Gwamnatin Katsina Ta Ware N1.5bn Domin Kawo Karshen Matsalar Rashin Tsaro

  • Gwamnatin Aminu Bello Masari na jihar Katsina ta ware zunzurutun kudi har naira biliyan 1.5 domin kawo karshen matsalar rashin tsaro
  • Masari ya sha alwashin baiwa hukumomin tsaro cikakken goyon baya domin yin maganin miyagu a jihar
  • A ranar Asabar ne aka yaye yan sa-kai 600 da za su taimakawa jami'an tsaro wajen fatattakar miyagu a lungu da sako na jihar

Katsina - Gwamnatin jihar Katsina ta ce ta ware kudi naira biliyan 1.5 domin yakar rashin tsaro a jihar.

Gwamnan jihar, Aminu Masari, ne ya bayyana hakan yayin bikin yaye yan sa-kai 600 a kwalejin hukumar tsaro ta NSCDC a ranar Asabar, Daily Trust ta rahoto.

Masari, wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Muntari Lawal, ya jinjinawa yan sa-kai wadanda suka dauki alkawarin zuwa kowani lungu da sako na jihar don taimakawa jami’an tsaro a yaki da fashi da makami, garkuwa da mutane da sauran laifuka.

Kara karanta wannan

Gwamna Soludo ya Wanke Fulani, Ya Bayyana Wadanda ke Assasa Rashin Tsaro a Anambra

Bello Masari
Gwamnatin Katsina Ta Ware N1.5bn Domin Kawo Karshen Matsalar Rashin Tsaro Hoto: The Sun
Asali: Facebook

Gwamnan ya jadadda jajircewar gwamnatinsa na taimakawa hukumomin tsaro da mutanen da suka sadaukar da kansu don taimakawa jihar a yaki da rashin tsaro.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Ya ce:

“Gwamnatina ba za ta yi kasa a gwiwa ba a kokarinta na taimakawa hukumomin tsaro, kungiyoyi da kuma mutane masu mutunci a yaki da rashin tsaro a jihar.”

A nashi jawabin, mai ba gwamnan shawara kan tsaro, Alhaji Ibrahim Katsina, ya ce yan sa-kai 600 sun kasance maza da mata masu matukar mutunci da kwalayen karatu da suka hada da NCE, Difloma, Digiri, Digir-gir da kuma digirin digir-gir, rahoton Premium Times.

A jawabinsa, kwamandan kwalejin NSCDC, Babangida Abdullahi, ya ce an horar da mutane kimanin makonni biyu a kwalejin kan makamai da sauran dabaru na yadda za a magance rashin tsaro.

Kara karanta wannan

An Haramta Amfani Da 'Mini Skirt' A Matsayin Unifom A Makarantun Wata Jihar Kudancin Najeriya

Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 1, Sun Sace Manoma 3 A Kaduna

A wani labarin kuma, mun ji cewa yan bindiga sun yi garkuwa da manoma uku yayin da suka kashe wani mutum daya a garin Kurgin Gabas da ke yammacin karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna.

Kungiyar ci gaban masarautar Birnin wato BEPU ta ce tun a ranar 1 ga watan Satumba yan bindiga suka toshe babban titin Birnin-Gwari-Funtua sannan suka kwace motoci fiye da 30 ciki harda manyan motocin daukar kaya, The Nation ta rahoto.

Kungiyar BEPU a cikin wata sanarwa da shugabanta, Ishaq Usman Kasai ya saki, ta kuma bayyana cewa matafiya da dama da aka sace a ranar 1 ga watan Satumba har yanzu ba a sako su ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng