Da dumi-dumi: Kwankwaso ya zabi fasto matsayin mataimaki a zaben 2023 mai zuwa

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya zabi fasto matsayin mataimaki a zaben 2023 mai zuwa

Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa dan takararta na shugaban kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, ya zabi Bishop Isaac Idahosa a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 mai zuwa.

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter a ranar Alhamis inda ta rubuta cewa:

“Mataimakin shugaban kasanmu Fasto Bishop Isaac Idahosa daga jihar Edo.”
Dan takarar NNPP ya zabi abokin gami
Da dumi-dumi: Kwankwaso ya zabi fasto matsayin mataimaki a zaben 2023 mai zuwa | Hoto: 0fficialNNPPng
Source: Twitter

Tribune Online ta ce ta ruwaito cewa, Bishop Isaac Idahosa daga jihar Edo babban Fasto ne a cocin God First Ministry, wanda aka fi sani da Illumination Assembly da ke da hedikwatara Lekki LLC, Ajah, Legas.

Zabo faston dai na zuwa ne bayan rade-radin da ke yawo na cewa Kwankwaso na neman zabo tsohon gwamnan Anambra Peter Obi a matsayin abokin takara.

Kara karanta wannan

Daga komawa Jam’iyyar APC, Orubebe ya samu mukami mai tsoka a zaben 2023

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng