Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja

Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja

  • Wasu tsagerun yan bindiga sun kai sabon kazamin hari jihar Neja, sun kashe aƙalla mutum uku kuma sun sace wasu sama da 30
  • Rahoto ya nuna cewa maharan sun kwashe tsayin lokaci suna aikata ta'adi kan mutane, sun kona gidaje a harin na kauyen Garin Gidigore
  • Ƙauyen da lamarin ya faru a yankin karamar hukumar Rafi ba shi da nisa da garin Birnin Gwari na jihar Kaduna

Niger - Miyagun yan bindiga sun kai wani mummunan hari yankin karamar hukumar Rafi da ke jihar Neja, arewa maso tsakiya a Najeriya.

Leadership ta ruwaito cewa yayin harin, yan bindigan sun kashe aƙalla mutum uku kuma suka sace mazauna 30 a ƙauyen Garin Gidigore, ƙaramar hukumar Rafi a Neja.

Harin yan bindiga a Neja.
Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja Hoto: channelstv.com
Source: UGC

Bayanai sun nuna cewa ƙauyen Garin Gidigore na da nisan kilomita kalilan zuwa garin Birnin Gwari a jihar Ƙaduna, yankin da yan bindiga ke da sansanoni daban -daban a dazukan da suka haɗa iyaka.

Kara karanta wannan

Kano: Majalisar Dokoki Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Naira Biliyan 10

Haka nan, rahotanni sun bayyana cewa yan bindigan sun kwashe dogon lokaci suna aikata mummunar manufar su kan mazauna ƙauyen a harin ranar Litinin da daddare.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bayan kashewa da sace wasu mutane maharan sun kona gidajen al'umma yayin da suke cin karen su babu babbaka a ƙauyen.

Yan bindiga sun sace mutum 50 a Zamfara

Wannan na zuwa ne yan kwanaki kaɗan bayan wasu yan bindiga sun yi awon gaba da wasu baƙi da suka halarci ɗaura aure a jihar Zamfara.

Yan ta'addan sun tuntuɓi iyalan waɗan sa suka yi garkuwa da su kuma sun bukaci a tattara musu maƙudan kuɗi da suka kai miliyan N145m a matsayin fansa.

Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya ce gwamnatinsa zata yi duƙ me yuwuwa don tabbatar da mutanen sun kuɓuta cikin ƙoshin lafiya.

A wani labarin kuma Bayan wani kazamin artabu, Sojoji sun samu gagarumar nasara kan yan ta'adda a Borno

Jami'an tsaro sun yi nasarar halaka yan ta'addan kungiyar ISWAP da dama a yankin Gurzum da ke jihar Borno.

Kara karanta wannan

Yan Bindiga Sun Bi Tsohon Kwamishina Har Gidansa Sun Sace Shi a Adamawa, Sun Bindige Mutum 2 Har Lahira

Hukumar sojojin Najeriya, ranar Laraba da safe, ta bayyana cewa dakarun sun lalata kasuwa da sansanin yan ta'addan yayin samamen.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262