Pantami Zai Jagoranci Taron Duniya Na Ƙungiyar Sadarwa Ta Shekarar 2022

Pantami Zai Jagoranci Taron Duniya Na Ƙungiyar Sadarwa Ta Shekarar 2022

  • Kungiyar Sadarwa ta Kasa da Kasa, ITU, ta zabi Isa Pantami, Ministan sadarwar Najeriya, a matsayin shugaban Taron Kungiyar Bayanai ta Duniya (WSIS) na 2022
  • Za a yi taron ne a hedkwatar Kungiyar sadarwa ta kasa da kasa da ke Geneva cikin Kasar Switzerland kamar yadda hadimin ministan na harkar bincike da ci gaba, Dr Femi Adeluyi ya bayyana a wata takarda
  • Ya ce an bayyana wa ministan wannan nadin ne ta wata wasika wacce Sakatare Janar na ITU, Houlin Zhao ya aiko masa kuma hakan ya biyo bayan dagewarsa da iliminsa a bangaren sadarwa

Ministan Sadarwa, Isa Pantami zai jagoranci taron Kungiyar Bayanai ta Duniya ta shekarar 2022 bisa nadin da Kungiyar Sadarwa ta Kasa da kasa (WSIS) ta 2022 ta yi masa, TVC News ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Ministan Buhari Da Ya Yi Murabus Don Takarar Gwamna Ya Janye Takararsa

Za a yi taron ne a hedkwatar Kungiyar Sadarwar ta Kasa da Kasa da ke Geneva cikin Switzerland.

Pantami Zai Jagoranci Taron Duniya Na Ƙungiyar Sadarwa Ta Duniya Na Shekarar 2022
Pantami Zai Jagoranci Ƙungiyar Sadarwa Ta Duniya Na Shekarar 2022. Hoto: TVC News.
Asali: Twitter

Kamar yadda takardar da hadimin ministan na bangaren bincike da ci gaba, Dr Femi Aduluyi ya saki ta nuna, an sanar da ministan batun nadin na shi ne ta wata takarda wacce babban sakataren ITU, Houlin Zhao ya aika masa.

Nadin Pantami ya biyo bayan ganin jajircewarsa akan ci gaba a harkar sadarwa

An nada Pantami ne saboda jajircewarsa a hanyar bayanai da ilimin fannoni da kuma dagewarsa akan harkokin WSIS, kamar yadda Zhao ya shaida. Kuma sai da su ka yi bincike kwarai kafin su dauki matakin.

TVC News ta ruwaito cewa akwai manyan kusoshin da za su halarci taron ciki har da ministocin kasashen ITU.

Kara karanta wannan

'Batanci: Atiku Ya Ce Ba Shine Ya Wallafa Rubutun Sukar Kashe Ɗalibar Sokoto a Shafinsa Ba

Kamar yadda takardar ta nuna:

“Nadin Pantami ya bai wa Najeriya da kuma Nahiyar Afirka wata babbar dama ta taka rawa a bangaren WSIS a shekararta ta 20, wanda an fara taron ne tun 2003 kuma an ci gaba da yi duk shekara.”

Manuniya ta nuna cewa duniya ta lura da ci gaban da Najeriya ta samu a fannin sadarwa

Takardar ta ci gaba da bayyana cewa:

“Alamu sun nuna cewa duniya ta ga yadda bangaren sadarwa ya bunkasa a Najeriya karkashin shugabancin Ministan. Hakan ya sa Pantami ya mika godiyarsa ga Shugaba Muhammadu Buhari akan kwarin gwiwar da ya ke ba shi a bangaren sadarwa.
“Fannin WSIS da hadin gwiwar kungiyoyin UN sun samar da damar bibiyar bayanai da kuma bincike tun shekara 2005. WSIS wacce ITU, UNESCO, UNDP da UNCTAD su ke sarrafawa da hadin gwiwar kungiyoyin majalisar dinkin duniya, ciki har da FAO, ILO, ITC, UNDESA, UNICEF, UNIDO, UNITAR, UNHCR, UNODC, UNEP, UPU, UN Tech Bank, WMO, WIPO, WHO, WFP, Kungiyar matan UN da sauransu.”

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164