Wankan Sallah: Hotunan Buhari, mukarrabansa da danginsa a ranar karamar sallah

Wankan Sallah: Hotunan Buhari, mukarrabansa da danginsa a ranar karamar sallah

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya halarci filin idin barikin Mambila a babban birnin tarayya Abuja
  • Shugaban dai ya bi sahun sauran musulmin Najeriya ne wajen gudanar idin karamar sallah ta shekarar 2022
  • Hotuna sun nuna shugaban tare da danginsa, iyalansa da wasu mukarrabansa jim kadan bayan idar da sallar

FCT, Abuja - Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bi sahun sauran musulmi a Najeriya, ya harkaci sallar idi a babban birnin tarayya Abuja.

Wata sanarwar da hadimin shugaban kasa, Buhari Sallau ya fitar ta shafin Facebook ta nuna hotunan shugaban lokacin da ya halarci sallar a barikin Mabila da ke Abuja a yau Litinin, 2 ga watan Mayu.

Hotunan sun nuna shugaban cikin farin ciki, yana daga wa jama'a hannu.

Kara karanta wannan

'Batanci: Bayan Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Deborah a Sokoto, Osinbajo Ya Yi Magana Da Kakkausar Murya

Buhari a sallar idi
Wankan Sallah: Hotunan Buhari da dangi a ranar karamar sallah | Hoto: Buhari Sallau
Asali: Facebook

Wani yankin sanarwar ya ce:

"Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya halarci Sallar Eid Al-Fitr a barikin Mambila, Abuja ranar 2 ga Mayu, 2022."

Hakazalika, sanarwar ta kuma nuno shugaban tare da danginsa; a fadar shugaban kasa bayan dawowarsu daga sallar idin da aka gudanar yau.

Sanarwar ta ce:

"Shugaba Buhari tare da uwargidan shugaban kasa Aisha Buhari da wasu 'ya'yansu, jikoki, da 'yan uwansu bayan halartar Sallar Idin Sallah a barikin Mambila, Abuja ranar 2 ga Mayu, 2022."

Baya ga ganawa da daniginsa bayan sallar, shugaban ya kuma gaisa da wasu mukarabbansa da jiga-jigan gwamnatin Najeriya.

A cewar Buhari Sallau:

"Shugaba Buhari tare da wasu mukarrabansa bayan halartar Sallar Eid Al-Fitr a barikin Mambila, Abuja ranar 2 ga Mayu, 2022."

Kalli hotunan a kasa:

Shirin 2023: Yahaya Bello ya gana da Buhari domin nuna masa fom din takarar shugaban kasa

Kara karanta wannan

2023: Jerin ministocin da suka yi murabus bayan umurnin Shugaba Buhari

A wani labarin na daban kun ji cewa, Shugaban kasa Muhammadu Buhari karbi bakuncin gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello a fadarsa da ke Aso Rock Villa da ke Abuja.

Ganawar tasu ta zo ne daidai lokacin da gwamnan ya sayi fom din tsayawa takarar shugaban kasa a jam'iyyar APC mai mulki gabanin zaben fidda gwani.

Fadar shugaban kasa ta ce, gwamnan ya gana da Buhari a yau Alhamis 28 ga watan Afrilu, kamar yadda hadimin shugaba Buhari ya yada wasu hotunan shugaban da gwamnan ta shafin Twitter.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.