Wutar lantarkin kasa ta sake lalacewa, Legas, Abuja Kaduna da wasu jihohi na cikin duhu

Wutar lantarkin kasa ta sake lalacewa, Legas, Abuja Kaduna da wasu jihohi na cikin duhu

  • Karo na uku cikin wata guda, tushen wutar lantarki Najeriya ya sake lalacewa gaba daya
  • Gwamnatin taayya ta bayyana cewa yanzu haka tana bincike kan abinda ya haddaa wannan lalacewa na wuta
  • Ma'aikatar wutar lantarki ta kasa ta ce barna da ake mata a hasumiyar rarrabe wutar lantarki ce ke janyo lalacewar wutar kasar nan

Kamfanonin rarraba wutar lantarki a Najeriya sun bayyana dalilin da ya sa wuta ta dauke a fadin tarayya ranar Juma'a, 9 ga watan Afrilu, 2022.

Mazauna Legas, Abuja, Kano, Kaduna da sauran jihohi sun ce tun da aka dauke wuta har yanzu babu.

Akalla kamfanoni uku sun saki jawabin tabbatar da hakan a shafukan ra'ayi da sada zumuntarsu.

Sun ce tushen wutan Najeriya gaba daya ne ya lalace misalin karfe 6:30 na yammacin Juma'a.

Kara karanta wannan

Matsalolin da Najeriya ke fuskanta alamun daukaka ne, In ji dan majalisa daga arewa

Kamfonin da sukayi sanarwa sun hada da na Legas Eko Disco, Abuja Disco, Kano Disco da Kaduna Disco.

Kamfanin rarraba wuta na Legas, Eko Disco yace:

"Ya ku kwatamominmu, muna sanar da ku cewa wutar kasa ta lalace daga karfe 6:30 na yammacin Juma'a, 8 ga Afrilu, 2022. Abokan harkallarmu na duba yadda za'a gyara nan ba da dadewa ba."

Kamfanin rarraba wuta na Abuja AEDC yace:

"Ku sani cewa rahsin wutan da kuke fuskanta sakamakon lalacewar wuta daga matattara ta kasa ne. Wutan ya lalace misalin karfe 6:30 da 8:50 na yammacin Juma'a."

Kamfanin rarraba wutan dake baiwa Kano, Katsina da Jigawa wuta kuwa yace:

"Muna sanar da ku dalilin rashin wuta. Muna baku hakuri bisa wannan abu."

Kara karanta wannan

Daga karshe, FG ta bankado abinda ke kawo lalacewar wutar lantarkin Najeriya

Barna a hasumiyar rarrabe wutar lantarki ce ta ka ga lalacewar wutar Ƙasa, FG

Ma'aikatar wutar lantarki ta tarayya a ranar Asabar ta ce lalacewar wutar lantarkin kasar nan ya biyo bayan barna da ake yi wa kasar a hasumiyar rarrabe wutar lantarkinta.

Jawbain yace:

"Karin bayani kan takarda da muka saki ga manema labarai, muna son sanar da jama'a cewa dalilin rashin wutan nan shi ne ayyukan mabarnata masu barna a hasumiyar rarrabe wutar lantarki da ke Odukpani Ikot Ekpene wanda yasa aka rasa 400MW na wutar da ake samu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel