Bidiyon matan gwamnoni a ziyarar Aisha Buhari da suka yi Dubai,sun bata kek na bazday

Bidiyon matan gwamnoni a ziyarar Aisha Buhari da suka yi Dubai,sun bata kek na bazday

  • Matan gwamnoni sun kai wa Aisha Buhari ziyara a Dubai tare da kek suna taya ta murnar zagayowar ranar haihuwarta a wani bidiyo
  • Matan sun rera mata waka, yayin da hasken kamara ya haska ko ina a kasaitaccen dakin da aka sauki bakin daga Najeriya
  • 'Yan Najeriya da dama sun yi mamakin cewa gwamnatin ce ta dauki nauyin tafiyar mayalwatan matan gwamnonin ba

A wani bidiyo da yayi yawo a kafafen sada zumunta, an nuna ziyarar da matan gwamnoni suka kai wa Aisha Buhari a Dubai tare da kek.

Suna taya ta murnar zagayowar ranar haihuwarta, wanda ya jawo cece-kuce daga 'yan Najeriya da dama a kafar sada zumuntar zamani ta Twitter, a lokacin da ake tsaka da karancin man fetur da yajin aikin ASUU.

Bidiyon matan gwamnoni a ziyarar Aisha Buhari da suka yi Dubai,sun bata kek na bazday
Bidiyon matan gwamnoni a ziyarar Aisha Buhari da suka yi Dubai,sun bata kek na bazday. Hoto daga @henryshield
Source: Twitter

Legit.ng ta lura da cewa, bikin zagayowar ranar haihuwar matar shugaban kasar na asali a watan Janairu ne, kuma a sirrance take shagalin.

Kara karanta wannan

Sabon jidali: Tallafin mai zai karu kan FG yayin da farashin mai ya tashi zuwa $112.7 kan kowacce ganga

Dukkan matan gwamnonin sun rerawa Aisha Buhari waka. Matan sun jeru a kayataccen dakin, inda suke tohowa zuwa ga Aisha a jere, suna rera mata wakar murnar zagayowar ranar haihuwar ta.

Fuskar su na bayyana farin ciki a hotuna, yayin da kamara ke haska kowanne lungu da sako na dakin, a lokacin da fuskar matar shugaban kasar ke dauke da murmushi da annashuwa, sannan ta rungume wasu daga cikin su.

Wannan bidiyon ya tattara daruruwan tsokaci, bayan @henryshield ya sake wallafa shi a Twitter.

Tsokacin 'yan Najeriya

Ga wasu daga cikin tsokacin:

@MummyKachi ta ce: "Tsananin rashin daraja, Uwar wasu."
@RealMrKay ya ce: "Ba ni da matsala idan Aisha Buhari ta yi murnar zagayowar ranar haihuwarta. Damuwa ta shi ne yadda suka mayar da Dubai babban birnin Najeriya. A Najeriya ne kadai matar shugaban kasa za ta yi fatali da kasar ta zuwa wata wawuyar kasa."
@Niellsbaba ya ce: "A wurin su babu yajin aiki, tunda bai shafi yaran su ba."

Kara karanta wannan

Budurwa ta gwangwaje matashi dake doguwar tafiya zuwa makatanta da dalleliyar mota

@MayorDeWriter ya ce: "Kawai saboda kek! Kusan su 12 suka kwashi jiki suka tafi Dubai! cabdi jam."
@Yusuf__jr ya ce: "Bayan kallon wannan bidiyon, za ka yi zaton wadanda suke mulka suna cikin farinciki."
@PapaEngagement ya ce: "Maganar gaskiya ba ni da matsala da wannan, tsaka-tsakin 'yan Najeriya da dama suna zuwa Dubai, US da sauran kasashe don wannan dalilin. A bayyane yake tana da kudin da za ta da kuma kudin Najeriya. Amma me zai sa matan gwamnoni tafiya har dubai don su bata kek?"

Hotunan 'ya'yan Buhari a wani taro tare da 'dan takarar shugabancin kasa

A wani labari na daban, gagarumin taron karramawa da bayar da lambar yabo da kungiyar 'yan jarida mata ta Najeriya ta shirya a ranar Alhamis da ta gabata ya samu halartar manyan mutane a sassa daban-daban na fadin kasar nan.

An shirya wannan taron ne domin karrama nasarorin uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, wacce ta samu wakilcin 'ya'yanta mata, Halima Buhari-Sheriff da Zahra Buhari-Indimi.

Kara karanta wannan

2023: Dattawan Arewa Sunyi Taro, Sun Yanke Shawarar Goyon Bayan Igbo Ya Maye Gurbin Buhari

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng