Da dumi: Mutum 2 sun hallaka, an yiwa wasu jina-jina a zaben deleget na PDP

Da dumi: Mutum 2 sun hallaka, an yiwa wasu jina-jina a zaben deleget na PDP

  • Jam'iyyar PDP a jihar Osun na gudanar da zaben deleget da zasu yi zabi wanda za'a baiwa tutar jam'iyyar a zaben gwamna
  • Wannan zabe ya rikide ya koma rikici inda aka fara rashin rayuka kuma wasu sun jigata
  • Kawo yanzu Alkalin zaben, Gwamnan jihar Adamawa, Ahmad Fintiri, basu isa wajen tattara zabe ba

Osogbo - Akalla mutum biyu sun rasa rayukansu yayinda da dama suka jikkata a zaben deleget na jam'iyyar People’s Democratic Party PDP dake gudana a jihar Osun.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, Yemisi Opalola, ta tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Laraba a Osogbo, TVCNews ta ruwaito.

A cewarta, an kashe wani matashi mai suna Toheeb Mutallib a Oke Oba, Agberire a karamar hukumar Iwo, yayinda aka kashe wani dan jam'iyyar siyasa Aremu Olamide a Ipetumodu, karamar hukumar Ife-North.

Kara karanta wannan

Ministoci da Shugabannin Gwamnatin da ke daf da asarar kujerunsu a sabuwar dokar zabe

Rikici
Da dumi: Mutum 2 sun hallaka, an yiwa wasu jina-jina a zaben deleget na PDP Hoto: @tvcNews
Asali: Twitter

Wasu masu idanuwan shaida sun bayyana cewa an yiwa mutane da dama jina-jina yayinda yan daba suka kai hari garuruwa irinsu Ede, Osogbo, Odo-Otin, Olorunda, Iwo, da sauransu.

Hakazalika an bankawa mota wuta a Ipetumodu sakamakon rikici tsakanin yan daba.

Kawo yanzu Alkalin zaben, Gwamnan jihar Adamawa, Ahmad Fintiri, basu isa wajen tattara zabe ba.

Za'a zabi mutum uku-uku a gundumomin jihar 332 kuma su zasu kada kuri'a a zaben fidda gwanin dan takaran gwamna a ranar 7 ga Maris, 2022.

Da dumi: Mutum 2 sun hallaka, an yiwa wasu jina-jina a zaben deleget na PDP
Da dumi: Mutum 2 sun hallaka, an yiwa wasu jina-jina a zaben deleget na PDP
Asali: Twitter

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng