Majlisar koli ta Shari'ah ta nada Abdurrashid Hadiyatullahi matsayin shugaban ta

Majlisar koli ta Shari'ah ta nada Abdurrashid Hadiyatullahi matsayin shugaban ta

  • Majalisar kolin kotun shari’ar Musulunci ta Najeriya (SCSN) ta nada AbdurRashid Hadiyatullah a matsayin shugabanta
  • Majalisar ta sanar da nadin nasa ne a ranar Litinin bayan kammala wani taro wanda suka yi a garin Kaduna
  • Nadin Hadiyatullah ya biyo bayan mutuwar Ibrahim Ahmed Datti, tsohon shugaban SCSN da ya rasu a jihar Kano

Majalisar koli ta shari’ar musulunci ta Najeriy, (SCSN) ta sanar da nada AbdurRashid Hadiyatullah a matsayin sabon shugaban ta.

TheCable ta ruwaito cewa, majalisar ta sanar da nadin ne ranar Litinin bayan kammala wani taro wanda su ka yi a Kaduna.

Majlisar koli ta Shari'ah ta nada Abdurrashid Hadiyatullahi matsayin shugaban ta
Majlisar koli ta Shari'ah ta nada Abdurrashid Hadiyatullahi matsayin shugaban ta. Hot daga thecable.ng
Asali: UGC

Nadin Hadiyatullah ya biyo bayan kwanaki kadan da mutuwar Ibrahim Ahmad Datti, tsohon shugaban SCSN, TheCable ta ruwaito.

Kamar yadda majalisar ta saki a wata takarda, Hadiyatullah ya rike kujerar mataimakin shugaban majalisar inda ya yi aiki tare da marigayi shugaban.

Kara karanta wannan

Khadijat yar shekara 38 ta bayyana shirinta na maye gurbin shugaba Buhari a 2023

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Majalisar ta shiga damuwa sakamakon rashin daya daga cikin jagororinta, Ibrahim Datti Ahmed, wanda har ya rasu yana kan kujerar shugaban majalisar. Muna masa fatan samun rahama da kuma Aljannar Firdausi,” kamar yadda takardar tazo.
“Yayin da muke takaicin wannan rashin, tare da mika dukkanin godiya ga Allah tare da bin dokar kundin tsarin mulki, Sheikh AbdurRashid Hadiyatullah, wanda shi ne mataimakin shugaban majalisar, ya zama shugaban majalisar koli ta shari’ar musuluncin Najeriya.
“Mu na fatan Allah SWT ya ba shi fasaha da jagoranci wurin isar da manufar majalisar musamman samar da hadin kai da ci gaba al’umma.”

Allah ya yiwa tsohon Shugaban Majalisar koli ta Shari'a, Dr Datti Ahmad, rasuwa

A wani labari na daban, Allah ya yiwa tsohon Shugaban Majalisar koli ta Shari'a a Najeriya (SCSN), Dr Datti Ahmad, rasuwa ranar Alhamis a jihar Kano.

Kara karanta wannan

Ka tuna da alkawarin da ka dauka: 'Yan Arewa sun roki Buhari kada ya basu kunya a 2022

Diraktan tashar Sunna TV, Dr Abu Aisha Ibrahim Disina a jawabin ta'aziyyarsa ya bayyana cewa za'a yi Sallar jana'iza a Masallacin Al-Furqan dake Kano misalin karfe 10 na safe. Ya siffanta marigayin a matsayin dan gwagwarmayan kare Musulmai a Najeriya.

A cewarsa:

"Gwagwarmayar kare muradun Musulmai ba za ta manta da kai ba a Nigeria!! Janaza: 10:00am a Masallacin Alfurqan Kano. Allah ya karbi aiyukanka, Ya kai haske kabarinka, Ya sanya Aljannah ce Makomarka. Allah ka kiyayemu, mu 'yan baya, Ya sa mu cika da Imani."

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng