Karin Bayani: Yan ta'addan ISWAP sun gwabza da Mafarauta a Jihar Borno

Karin Bayani: Yan ta'addan ISWAP sun gwabza da Mafarauta a Jihar Borno

  • Rahoto ya bayyana cewa wasu da ake zargin mayakan ISWAP ne sun kai hari kauye a kudancin jihar Borno
  • Wata majiya ta bayyana cewa mafarauta a yankin kauyen sun tarbi yan ta'addan, inda suka yi ɗauki ba daɗi
  • Mamban kungiyar jami'an sa'kai, CJTF, ya bayyana cewa mayakan ISWAP sun ci karfin mafarautan sun shiga cikin ƙauyen

Borno - Wasu yan ta'adda da ake zargin mayakan kungiyar ISWAP ne na can sun farmaki wani kauye a kudancin Jihar Borno, kamar yadda Dailytrust ta rahoto.

Yan ta'addan sun farmaki kauyen Shallangba wanda ke kusa da Debiro a karamar hukumar Hawul, jihar Borno.

Sai dai rahotanni sun bayyana cewa mafarauta yan sa kai sun tarbi yan ta'addan, kuma sun fafata da juna yayin harin.

Jihar Borno
Yanzu-Yanzu: Yan ta'adda na can sun buɗewa mutane wuta a wani gari a jihar Borno Hoto: channelstv.com
Source: UGC

A cewar wata majiya, yan ta'addan sun kai hari ƙauyen a kan motoci, inda suka bude wuta kan mai uwa da wabi yayin da mutanen kauyen suke kokarin tserewa zuwa cikin jeji.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: An Kashe Fitaccen 'Dan Kasuwan Najeriya a Afirka ta Kudu

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Wani mamban tawagar jami'an tsaron sa kai (CJTF) yace yan ta'addan sun fi karfin mafarautan, yanzu haka suna cikin ƙauyen.

A ranar Lahadi da maraice, wasu yan ta'adda suka kai hari ƙauyukan Debiro, wanda ya haɗa iyaka da kananan hukumomin Biu da Hawul na jihar Borno.

A kwanakin bayan nan dai, yan ta'addan dun matsa da kai hare-hare jihar Borno, inda a wani harin suke sace matafiya.

A wani labarin na daban kuma Fadar Shugaban ƙasa ta bayyana abinda Buhari ke yi domin kawo karshen kalubalen tsaro a faɗin Najeriya

A kullum shugaba Buhari sai ya yi maganar mutanen da ake kashewa tare da yi musu addu'a, inji fadar shugaban kasa.

Malam Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar, yace shugaba Buhari yana damuwa fiye da tunani kan halin rashin tsaro da ake ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: