Bidiyo da hotunan gasar karatun Al-Kur'ani da rundunar 'yan sanda ta shirya a Kano a tsakanin jami'ai

Bidiyo da hotunan gasar karatun Al-Kur'ani da rundunar 'yan sanda ta shirya a Kano a tsakanin jami'ai

  • Rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta shirya gasar karatun Al-Kur'ani a tsakanin jami'anta da ke aiki a jihar Kano
  • Rahoton da muke samu ya bayyana cewa, a halin yanzu ana ci gaba da gasar, wanda za a kammala yau Alhamis
  • An gudanar da gasar karatun ne a karkashin jagorancin kwamishinan 'yan sandan jihar Kano, CP Sama'ila Shu'aibu Dikko

Kano - Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta shirya gudanar da gasar karatun Al'Kur'ani tsakanin jami'an 'yan sandan da ke aiki a jihar Kano.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka a cikin wani bidiyo da ya yada a shafinsa na Facebook a ranar Laraba 17 ga watan Nuwamba, 2021.

Bidiyon gasar karatun Al-Kur'ani da rundunar 'yan sanda ta shirya a Kano a tsakani jami'ai
Lokacin gudanar kasar karatun Al-Kur'ani na 'yan sanda a jihar Kano | Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Source: Facebook

A cewar Kiyawa, ana gudanar da gasar karatun ne a hedkwatar 'yan sanda da ke Bompai a jihar Kano, a karkashin jagorancin kwamishinan 'yan sandan jihar, CP Sama'ila Shu'aibu Dikko.

Kara karanta wannan

Harin ISWAP: Lamari ya yi zafi, sojoji sun sanya dokar hana fita a yankin Borno

A cikin bidiyon, Legit.ng Hausa ta gano lokacin da Kiyawa yake yiwa jama'a bayanin abin da ke faruwa, inda aka nuna jami'in dan sanda na karanta Al-Kur'ani a gaban alkalan gasa.

Kalli bidiyon:

A wani sabon bidiyon da Kiyawa a sake da safiyar ranar Alhamis, ya bayyana cewa, ana kokarin kammala gasar Al-Kur'anin, kuma nan kusa kadan za a bayyana sakamakon gasar.

Kana, Legit.ng Hausa ta tattaro hotunan lokacin da ake gudanar da gasar, wanda jami'in hulda da jama'a, Abdullahi Haruna Kiyawa ya yada a Facebook.

Kalli hotunan:

Yadda tsohon Mataimakin Gwamnan jihar Kano ya canza gidan siyasa sau 6 a shekara 7

A wani labarin, Jaridar Daily Trust ta rahoto Farfesa Hafizu Abubakar yana bayanin abin da ya sa ya bar tsagin mai girma gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya bi tawagar G7.

Hafizu Abubakar yace ya bi tawagar masu adawa da tsagin gwamnati ne domin su ne a kan gaskiya, yace suna tafiya da kowa a siyasance yadda ya kamata.

“Maganar gaskiya abin da ke faruwa a jam’iyyar APC, abin takaici ne. Ba haka mu da duk magoya bayanmu, muka sa rai ba.” - Hafizu Abubakar.

Kara karanta wannan

Har bayan wata 7, an kasa sasanta rikicin Kwankwaso da Wali a PDP

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng