Da Dumi-Dumi: Rikici ya barke tsakanin yan Keke-Napep da jami'an yan sanda, An bindige mutum daya

Da Dumi-Dumi: Rikici ya barke tsakanin yan Keke-Napep da jami'an yan sanda, An bindige mutum daya

  • Direbobin Keke-Napep sun mamaye kan hanya domin nuna fushinsu kan kisan da wani ɗan sanda ya yi wa ɗayansu a jihar Legas
  • Rahotanni sun bayyana cewa sun fara wannan zanga-zanga ne bayan bindige ɗan Napep ɗaya har Lahira a bakin titi a yankin Meran
  • Kwamishinan yan sandan jihar, Hakeem Odumosu, ya tura jami'an sintiri zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya

Lagos - Yanzun haka direbobin Keke-Napep na can suna zanga-zanga a yankin Abule-Egba dake jihar Legas bisa zargin jami'an yan sanda da harbe ɗaya daga cikinsu.

Dailytrust tace direbobin Napep sun mamaye hanyoyi da safiyar Alhamis, inda suka toshe hanyar shiga da fita Anguwan Meran, wani yanki a Abule-Egba.

Masu zanga-zangar sun ɗauki wannan matakin ne domin nuna fushinsu kan yadda jami'an yan sanda ke cin mutuncinsu har takai ga harbi.

Kara karanta wannan

Babban malamin addinin musulunci ya sace ɗan uwansa, ya nemi a lale masa miliyoyi kudin fansa

Keke Napep
Da Dumi-Dumi: Rikici ya barke tsakanin yan Keke-Napep da jami'an yan sanda, An bindige mutum daya Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Meya faru aka kashe ɗan Napep?

Wasu na zargin cewa jami'in hukumar yan sanda ne ya daba wa direban Keke-Napep ɗin wuka yayin da wasu ke cewa bindige shi ya yi, kuma ya barshi nan kan hanya har ya mutu.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Rahotanni sun bayyana cewa rikicin dai tsakanin yan sanda da direbobin Napep ɗin ya faru ne a kan hanyar Command, Meran, Abule-Egba, ranar Alhamis.

Wane mataki hukumar yan sanda ta ɗauka?

Kakakin hukumar yan sanda rashen jihar Legas, Adekunle Ajisebutu, ya tabbatar da faruwar lamarin ta saƙon WhatsApp.

Ya kuma ƙara da cewa kwamishinan yan sanda na jihar Legas, Hakeem Odumosu, ya tura ƙarin jami'an yan sanda wurin domin kwantar da tarzomar.

Punch ta rahoto kakakin yan sandan yace:

"Kwamishinan yan sanda ya tura ƙarin jami'an sintiri zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya da doka da oda."

Kara karanta wannan

Aƙalla mutum 7 suka mutu yayin da miyagun yan bindiga suka kai harin farko yankin wannan jihar

A wani labarin kuma mun kawo muku Yadda wata yar bautar kasa NYSC ta mutu a Legas bayan ta guje wa matsalar tsaro a Borno

Mahaifiyar Zaynab Sanni Oyindamola, wata mambar NYSC ta samar wa ɗiyarta canjin wurin aiki daga jihar Borno saboda rashin tsaro.

Hakanan kuma mahaifiyar tana son ɗiyarta ta yi aiki a wuri mai tsaro kuma wanda bata sani ba, amma ashe hakan wata ƙaddara ce take kiranta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262