Da Dumi-Duminsa: Wani gini mai hawa-hawa ya sake kifewa a jihar Legas
- Rahoto daga jihar Legas ya bayyana cewa wani gini mai hawa-hawa ya kife awanni 24 bayan mai hawa sama da 20 ya ruguje
- Lamarin dai ya faru ne da safiyar Talata, kuma ginin ya rushe ne bayan wani mamakon ruwa da aka yi da dare
- Jami'ai hukumar bada agaji, NEMA, da sauran hukumomi na cigaba da aikin ceto a wurin gini mai hawa sama da 20
Lagos - Wani gini mai hawa biyu ya ruguje a yankin Anguwar Lekki dake jihar Legas, ranar Talata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Rahoto ya bayyana cewa ginin wanda ba'a kammala shi ba, ya rushe ne bayan a yi wani mamakon ruwa ranar Litinin da daddare.
Wannam na zuwa ne awanni 24 bayan dogon gini mai hawa sama da 20 ya rushe a yankin Ikoyi, na jihar ta Legas.

Kara karanta wannan
Yan bindiga sun kashe Limamin Masallacin Juma'a da yaki yarda a tafi da shi, sun sace yaransa

Asali: UGC
Halin da ake ciki wajen ceto mutane?
Jami'an hukumar agaji NEMA sun samu nasarar gano gawar mutum uku daga cikin dogon ginin da ya rushe a jihar Legas.
Hakanan an kuma ceto wasu mutunw da suke da sauran numfashi a gaba, suna asibiti ana kulawa da lafiyarsu.
Babban ginin, wanda ake cikin ginawa, ya ruguje ne a kan hanyar Gerald dake yankin Anguwar highbrow a jihar Legas.
Shugaban hukumar bada agajin gaggawa, NEMA, Ibrahim Farinloye, yace an matsar da gawarwakin zuwa ɗakin ajiye gawa mallakin gwamnatin jihar Leagas.
A wani labarin na daban kuma Bayan harin masallaci, yan Bijilanti sun kashe mutum 9, sun ƙona gidaje a wata rugar Fulani a jihar Neja
Rahoto ya nuna cewa maharan sun ƙone gidaje a wata rugar Fulani, bayan kashe dagacin Adogon Mallam da ɗan uwansa.

Kara karanta wannan
Gwamnan Legas ya kori daraktan kula da gine-gine bayan rugujewar bene mai hawa 22
Hukumar yan sanda ta tura jami'anta na musamman domin kame duk wani mai hannu a harin.
Asali: Legit.ng