Latest
Sheikh Isa Ali Pantami ya bayyana cewa mutane ne suka sanya shi shiga takarar gwamna a jihar Gombe. Ya fadi abubuwan da zai yi wa Gombawa idan ya zama gwamna.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kira gwamnan jihar Ondo, Lucky Orimisan Aiyedatiwa, zuwa fadarsa. Kiran na zuwa ne bayan an yi kashe-kashe a taron APC.
Kotun jihar Enugu ta yankewa wani fasto hukuncin kisa kan laifin kashe wani dalibin jami'a. Alkalin kotun ya ce abin takaici ne malamin addini ya kashe rai.
'Yan Najeriya sama da miliyan 1 sun yi rajistar katin zabe da hukumar INEC. Jihar Jigawa ce ta farko, yayin da Legas ta zo ta biyu, Sokoto na binta a baya sai Kano.
Shugabannin APC na jihar Adamwa sun garzaya har gidan gwamnati, sun gana da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yayin da ake rade-radin zai bar PDP zuwa APC.
'Yan bindiga sun kashe mutane 50 a Tungan Dutse, da ke jihar Zamfara. Mazauna yankin sun ce an yi watsi da gargaɗin su kafin harin ya auku a cikin watan Ramadan.
Ana ta ce-ce-ku-ce game da kudirin da wasu yan Majalisar Amurka suka gabatar wanda ya ambaci Rabiu Kwankwaso a cikin wadanda ake zargi da take hakkin kiristoci.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya zakulo limaman masallatan Juma'a 40, ya ba kowane sabuwar mota domin ci gaba da harkokin yada addinin musulunci.
'Yan bindiga sun kashe makiyaya 3 a Barkin Ladi, Filato a hanyarsu ta komawa gida daga sauraron tafsiri. Kungiyar MACBAN ta zargi 'yan kabilar Berom.
Masu zafi
Samu kari