Dubu Ta Cika: Iran Ta Cafke Masu Taimakon Amurka da Isra'ila a Yakin da Ake Yi

Dubu Ta Cika: Iran Ta Cafke Masu Taimakon Amurka da Isra'ila a Yakin da Ake Yi

  • Mahukunta a Iran sun tabbatar da cafke daruruwan mutane da ake zargi da cin amanar kasa ta hanyar wasu ayyukan da suke yi
  • Hakazalika, mahukuntan sun bayyana cewa za su ci gaba da cafke mutanen da ke marawa muradun Amurka da Isra'ila baya
  • Hukumar leken asiri ta bayyana cewa an samu makamai a hannun cikin mutanen da aka cafke, tare da yin kira ga jama'a su kai rahoton duk abin da ba su yarda da shi ba

​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Tehran, Iran - Hukumomin Jamhuriyar Musulunci ta Iran sun sanar da cafke karin daruruwan mutane a faɗin ƙasar.

Hakazalika sun sanar da gudanar da ayyukan kakkabe mutanen da suka bayyana a matsayin “maci amana” waɗanda ke mara wa muradun Amurka da Isra'ila baya.

Mahukunta sun cafke mutane a Iran
Sabon jagoran addini na kasar Iran, Mojtaba Khamenei Hoto: Reza B
Source: Getty Images

Tashar Aljazeera ta kawo rahoton cewa ma'aikatar leken asiri ta bayyana cafke mutanen a cikin wata sanarwa.

Kara karanta wannan

Iran ta kama ɗan leƙen asirin Isra'ila ana tsaka da yaƙi, an zartar masa hukunci

Mahukunta a Iran sun cafke wadanda ake zargi

Ta bayyana cewa an dakatar da ayyukan "ƙungiyoyin masu goyon bayan masarauta” guda 111 a cikin larduna 26 daga cikin 31 na Iran a daren Talata zuwa ranar Laraba, 17 ga watan Maris 2026.

An bayyana cewa mutanen da aka kama suna shirin kaddamar da ayyukan nuna adawa da tsarin mulkin addini na ƙasar wanda ya kifar da masarautar da Amurka ke goyon baya a juyin juya halin Musulunci na 1979.

An gudanar da bikin Nowruz a Iran

Al'ummar Iran sun shafe shekaru dubbai suna gudanar da bikin wuta da ake kira Chaharshanbe Suri a daren Larabar ƙarshe ta kowace shekara, domin maraba da sabuwar shekarar Farisa wato Nowruz.

Sai dai a wannan shekarar, hukumomi sun buƙaci masu goyon bayan gwamnati da su fito kan tituna don tabbatar da iko, yayin da jami'an tsaro ke kama duk wani mai adawa, a daidai lokacin da ake tsaka da yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran.

Kara karanta wannan

Iran ta yi ruwan bama bamai a tsakiyar Isra'ila bayan kisan Larjani, an kiɗima Yahudawa

An gano makamai a hannun wadanda ake zargi

Ma'aikatar ta yi ikirarin cewa an gano wasu makamai a hannun mutanen da aka kama, sannan ta sabunta kiran ta ga jama'a da su kai rahoton duk wani motsi da ba su yarda da shi ba, tashar Iranpress ta kawo labarin.

Wasu daga cikin daruruwan da aka kama a birnin Karaj da ke kusa da Tehran sun “ƙona hotunan tsohon jagoran addini da aka kashe tare da yi masa batanci,” wato Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a farkon yaƙin ranar 28 ga Fabrairun 2026.

Tun daga wannan lokacin ne aka zaɓi ɗan Khamenei, Mojtaba Khamenei, a matsayin sabon jagoran addini na Iran.

Iran ta cafke mutanen da take zargi
Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian Hoto: @drpezeshkian
Source: Twitter

Amurka da Iran na son sauya gwamnati

Amurka da Isra'ila, waɗanda suka ayyana kifar da gwamnatin Iran a matsayin ɗaya daga cikin manufofinsu, sun kasance suna farmakar tsarin tsaron cikin gida na dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC).

Shingayen bincike na dakarun Basij sun kasance suna shan luguden wuta daga jirage marasa matuƙa tsawon mako guda, yayin da aka tabbatar da kisan shugaban tsaro Ali Larijani a daren jiya, tare da wani babban mataimaki a majalisar tsaro ta kasa.

Kara karanta wannan

Iran ta 'ki hakura, ta taso Amurka a gaba game da kashe yan mata a makaranta

Isra'ila ta sha alwashin kashe Mojtaba Khamenei

A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar sojojin Isra'ila (IDF) ta sha alwashin ganin bayan sabon jagoran addini na Iran.

Rundunar IDF ta bayyana cewa za ta farauto tare da kashe sabon jagoran addini na Iran, Mojtaba Khamenei a duk inda yake.

Hakazalika, rundunar ta bayyana cewa za ta ci gaba da farmakar jami'an gwamnatin Iran har ta ga bayansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng