Bidiyo: Gwamnatin Saudiyya Ta Damke Wanda Yaje Umrah Don Sarauniya Elizabeth
- Wani Balarabe ya shiga harami gabatar da aikin Umrah don marigayiya Sarauniya Elizabeth II
- Jami'an tsaron Masallacin Harami sun cika hannu da shi kuma sunce zai gurfana gaban kuliya
- Duk da cewa ya halasta ayi umrah don wani, hakan bai halasta ga wanda ba Musulmi ba
Hukumomi a kasar Saudiyya sun damke wani mutumi da yayi ikirarin ya yi tattaki zuwa Makkah don yin aikin Umrah a madadin marigayiya Sarauniya Elizabeth II.
Mutumin dan kasar Yemen, a ranar Litnin ya wallafa bidiyon kansa a soshiyal midiya yana filin Harami.
Rike da wata farar riga da rubutu a kanta, ya yi addu'an Allah a jikan Sarauniya Elizabeth.
A rubuce kan rigar:
"Ina Umrah don Saraunia Elizabeth II, muna rokon Allah ya karbeta cikin salihan bayi."

Kara karanta wannan
Adamawa: An biyashi N5000 da kwanon Shinkafa 4 don yayi kisan kai, ya kashe mutum 1, ya bar daya na jinya
Bidiyon ya yadu a kafafen sada zumuntan Saudiyya inda mabia Tuwita suka bukaci a damkesa.
DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka
Gwamnatin kasar Saudiyya ta haramta zanga-zanga ko rike hoton wani don kamfe a cikin Haramin Makkah.
Duk da cewa ya halasta ayi umrah don wani Musulmi da yai mutu, hakan bai halasta ga wanda ba Musulmi ba irin Sarauniyar Elizabeth.

Asali: Twitter
An damkeshi
Jami'an tsaron Haramin Makkah sun damke mutumin wanda dan kasar Yemen ce, rahoton TRT.
Kafar yada labaran Saudiyya a ranar ta bayyana cewa:
"An damke wani dan kasar Yemen mazauni Saudiya wanda ya bayyana a bidiyo yana rike da tsumma cikin harami, hakan ya sabawa dokokin yin Umrah."
"An damkeshi kuma za'a wanzar da hukunci doka kansa."
Kalli bidiyon:
Sarauniyar Ingila, Elizabeth II Ta Rasu Tana da Shekaru 96
Kun ji labarin rasuwar sarauniyar Ingila Elizabeth II bayan 'yar gajiriyar rashin lafiya da aka sanar ta yi ranar Alhamis 8 ga watan Satumba.
Rahotanni daga majiyoyi sun shaida cewa, masarautar Ingila ta tashi bakin labarin jirkicewar lafiyar sarauniya, lamarin da yasa likitoci ke kai komo a kanta.
A wata sanarwar da masarautar ta Ingila ta fitar, an sanar da rasuwar sarauniyar da yammacin Alhamis.
Asali: Legit.ng