Dan Najeriya ya lashe gasar Al-Qur'ani a kasar Saudiya

Dan Najeriya ya lashe gasar Al-Qur'ani a kasar Saudiya

Wani mai aikin hajji daga jihar Kaduna, Malam AbdurRahman Ahmed Salis, ya lashe gasar karatun Al-Qur’ani mai girma da massalaci mai tsarki na garin Makka, kasar Saudiya.

Dan Najeriya ya lashe gasar Al-Qur'ani a kasar Saudiya
Dan Najeriya ya lashe gasar al-Qur'ani da akayi a kasar Saudiya

Da yake Magana da yan jarida a kasar Saudiya, Chiyaman na kungiyar karatun Al-Qur’ani na jihar Kaduna, De. Bello AbdulKadir, ya bayyana cewa AbdurRahman mai shekaru 24 a duniya ya sa kasar cikin alfahari da farin cikin a kasa mai tsarki.

A cewar sa, An dauki nauyin aikin hajjin AbdurRahman ne saboda ya zo na farko a lokacin gasar karatun al-Qur’ani na kasa baki daya na kamfanin Maltina, amma kuma yayi wani shiri na mussaman a massalaci mai tsarki bayan aikin hajji.

Abdulkadir ya bayyan cewa taron ya hada da karatun al-Qur’ani a cikin siga mai kyau da kuma karatun tajwidi na littafi mai tsarki.

KU KARANTA KUMA: Tanko yakasai yayi magana a kan Tinubu da Oyegun

An ba koma damar shiga shirin, ciki harda ma’aikatan masalaci mai tsarki, hukumomin tsaro da kuma mahajjata da kuma duk wanda yaga yana ra’ayin bunkasa iliminsa a kan Qur’ani:, ya ci gaba da cewa.

Chiyaman din kungiyar karatun Qur’anin ya kara da cewa a karshen taron, dan jihar Kaduna AbdurRahman Salis ya lashe kasar inda ya fito a matsayin dalibi mafi kokari an kuma basa takardun lambar yabo da dama.

A cewar sa, AbdurRahman ya taba wakiltan kasar Najeriya a gasar karatun Qur’ani na duniya a kasar Tanzania a cikin shekara ta 2013, Iran a shekara ta 2014 da kuma kasashen musulunci da dama, inda ya kawo farin ciki ga kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng