Kungiyar gamayyar jam’iyyun siyasa tace akwai shirin kawo matsala a zaben 2023
- Kungiyar CUPP tace akwai makarkashiya a game da zabe mai zuwa na 2023
- Ikenga Imo Ugochinyere yace akwai yiwuwar a ki amfani da na’urar zamani
- Kakakin kungiyar ya bayyana cewa ana ba ‘Yan majalisar tarayya cin hanci
Abuja - Kungiyar gamayyar jam’iyyun siyasar Najeriya, CUPP, ta sanar da jama’a cewa ta samu labarin kawo wa zabe mai zuwa na shekarar 2023 cikas.
A wajen wani taron manema labarai da aka shirya a garin Abuja, kakakin CUPP, Mista Ikenga Imo Ugochinyere yace akwai shirin a hana ayi adalci a zaben.
Leadership ta rahoto Ikenga Imo Ugochinyere yana cewa ba za a karasa sa hannu a dokar zabe ta yadda hukumar INEC za tayi amfani da na’urorin zamani.
Imo Ugochinyere yake cewa ana so da karfi da yaji a ki yin aiki da na’urori wajen tattara kuri’u.
Jaridar ta rahoto mai magana da bakin kungiyar yana cewa ana ba ‘yan majalisa cin hanci domin a ga an yi watsi da batun yi wa dokar zabe kwaskwarima.

Source: Facebook
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Mun samu kishin-kishin - Ikenga Imo Ugochinyere
“Bayanan da suke zuwa mana shi ne, ana hada wa da ba ‘kwamitocin ‘yan majalisa cin hanci cikin dare domin su ga ba a bari an yi amfani da na’ura a zabe ba.”
Ugochinyere yace ‘yan majalisa sun yarda su yi ta jan maganar yi wa dokar zabe garambawul har zuwa lokacin da za su tafi dogon hutu a shekara mai zuwa.
“Wannan cin mutunci ne ga ‘yan Najeriya, ganin cewa an fara aikin gyara dokar zabe tun shekarar 2016, kuma har bayan shekaru biyar ba a kammala ba.”
Kungiyar ta CUPP tace idan maganar ta kai lokacin, ba za a iya yi wa dokokin zabe wata kwaskwarima ba kamar yadda dokokin ECOWAS suka tanada.

Kara karanta wannan
Tauraron Nollywood ya shiga hannun Sojoji, ana zarginsa da ba ‘Yan ta’adda goyon baya
A madadin CUPP, Ugochinyere yace mutanen Najeriya ba za su yarda a hana hukumar INEC amfani da na’urorin zamani wajen gudanar da zaben na 2023 ba.
Uzor Kalu ya yi magana kan 2023
A makon nan aka ji Sanatan jihar Abia ta Arewa Orji Uzor Kalu ya na bayani cewa bai da sha’awar zama Shugaban Najeriya a 2023, amma jama’a su na tunzura shi.
Uzor Kalu yace yana so ne ya zarce a kujerar da yake ta ‘Dan Majalisar Dattawa ba ya rike kasa ba.
Asali: Legit.ng
