Saboda a murdewa APC zaben Gwamna ake shirin kafa dokar ta baci a Anambra inji PDP

Saboda a murdewa APC zaben Gwamna ake shirin kafa dokar ta baci a Anambra inji PDP

  • Jam’iyyar PDP ta maida martani a kan batun sa dokar ta-baci a jihar Anambra
  • Kakakin PDP ya zargi gwamnatin tarayya da shirin yin magudi a zaben gwamna
  • Kola Ologbondiyan ya fitar da jawabi, ya yi kira a kawo karshen matsalar tsaron

Abuja – Babbar jam’iyyar hamayya ta PDP tayi gargadi a kan kafa dokar ta-baci a jihar Anambra yayin da ake shirin gudanar da zaben sabon gwamna.

A wani jawabi da ya fitar, mai magana da yawun bakin PDP ta kasa, Kola Ologbondiyan, yace gwamnatin tarayya ta daina tunanin sa dokar ta-bacin.

Gidan talabijin na Channels TV ya rahoto sakataren yada labarai na jam’iyyar adawar yana zargin gwamnatin APC da kawo wannan domin a murde zabe.

Ologbondiyan ya yi wa jawabin take da Gwamnatin tarayya ta birne tunanin kakaba dokar ta baci a Anambra, yayin da ake shirin zaben 6 ga watan Nuwamba.

Kara karanta wannan

2023: CUPP ta samu kishin-kishin, zaben Shugaban kasa zai iya gamuwa da cikas

Jaridar Premium Times ta rahoto Ologbondiyan yana zargin APC da yunkurin tafka magudi a zaben sabon gwamnan ta yadda za ta kafa gwamnati a jihar.

Shugabannin APC
Buni, Buhari da 'Dan takarar APC a zaben Anambra Hoto: pmnewsnigeria.com
Asali: UGC

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Jawabin da Kola Ologbondiyan ya fitar

“Jam’iyyar PDP tayi imani cewa neman kafa dokar ta-baci a jihar Anambra, dabara ce ta gwamnatin APC ta yadda za ayi wa mutane murdiya, a murde zabe zaben gwamna domin APC da ‘dan takararta su samu nasara.”
“Jam’iyyarmu tana bukatar APC da gwamnatinta ta yi bayanin abin da ya jawo karu war rashin tsaro a jihar Anambra a lokacin da ake shirin yin zabe.”

Sakataren yada labaran na jam’iyyar PDP yace an dasa irin rikice-rikicen da ake gani a Anambra ne saboda jam’iyyar APC ta samu damar dare wa kan mulki.

PDP tace za a iya shawo kan matsalar tsaro ba tare da sa dokar ta-baci ba, tayi kira ga gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta APC tayi abin da ya kamata.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Manyan PDP sun amince dan arewa ya shugabanci jam'iyyar

A karshen jawabin, jam’iyyar adawar tayi kira ga mutanen jihar Anambra su kwantar da hankalinsu.

Magoya baya suna taya Tinubu kamfe

A farkon makon nan aka ji fastocin babban jigon jam'iyyar APC a kudu maso yammacin Najeriya, Bola Ahmed Tinubu sun fara cika wasu lungunan jihar Legas.

An ga fastocin Bola Tinubu a Ojota, Maryland, Ketu Ikeja, da Lagos Island. Abin tambayar shi ne wa zai zama abokin takarar babban ‘dan siyasar a APC a 2023.

Asali: Legit.ng

Online view pixel