Hotunan Mutane 5 Masu Garkuwa Da Mutane Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi

Hotunan Mutane 5 Masu Garkuwa Da Mutane Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi

  • Mafarauta sun yi nasarar kama wasu maza biyar da ake zargi masu garkuwa ne a jihar Kogi
  • Wadanda aka kama din sun hada da Tukur Saleh, Ahmadu Sanni, Yusuf Sanni daga Bauchi sai Abubakar Saleh (Baba Wuro) da Isah Saleh daga jihar Kano
  • Hon Abdulraheem Ohiare Ozovehe, shugaban karamar hukumar ya tabbatar da kama bata garin ya kuma ce an mika su hannun jami'an tsaro

Jihar Kogi - Kwararrun mafarauta a karamar hukumar Okehi a jihar Kogi sun yi nasarar kama mutane biyar 'yan kungiyar masu garkuwa da mutane, LIB ta ruwaito.

An kama mutane biyar din da ake zargi a safiyar ranar Talata a Atami, wani gari da ke wajen Osara a ranar Talata, 27 ga watan Satumban shekarar 2021.

Kara karanta wannan

Tsohon Saurayi ya aikewa Ango tsaffin hotunan amaryarsa kan ta tuba, aure ya mutu

Hotunan Mutane 5 Masu Garkuwa Da Mutane Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi
Masu Garkuwa Da Mutane Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi. Hoto: LIB
Asali: Facebook

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

King Habib, babban hadimi ga shugaban karamar hukumar Okehi a bangaren watsa labarai, Hon Abdulraheem Ohiare Ozovehe ya tabbatar da kama wadanda ake zargin, yana mai cewa tawagar sun dade suna adabar mutane a titin Okene-Lokoja da Okene-Auchi a jihar Kogi State.

Sanarwar ta ce a halin yanzu an mika wadanda ake zargin a hannun jami'an tsaro yayin da ake cigaba da zurfafa bincike domin kwato muggan makamai da suke da shi, rahoton LIB.

Hotunan Mutane 5 Masu Garkuwa Da Mutane Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi
Masu Garkuwa Da Mutane Biyar Da Ƙwararrun Mafarauta Suka Kama a Kogi. Hoto: LIB
Asali: Facebook

Wadanda aka kama din sun ne: Tukur Saleh, Ahmadu Sanni, Yusuf Sanni, dukkansu daga Bauchi; Abubakar Saleh (Baba Wuro) da Isah Saleh, su kuma daga jihar Kano.

Hon Ohiare ya ce:

"Ba za mu yi kasa a gwiwa ba wurin ganin mun kawar da bata gari daga karamar hukumar Okehi da kewaye."

Kara karanta wannan

Yadda jami'an tsaron UNIMAID suka afka dakunan kwanan dalibai mata, suka damke masu zanga-zanga

Sarkin Katsina ya barranta da matsayar Sheikh Gumi: Kisa ya dace da ƴan bindiga ba tattaunawa da su ba

A wani labarin daba, mai martaba Sarkin Katsina ya ce tunda ƴan bindiga sun zaɓi su rika kashe mutane 'suma bai dace a bar su da rai ba'.

Sarkin na Katsina, Abdulmuminu Usman ya ce ba abin da ya dace da ƴan bindigan da ke kashe mutane a arewa maso yamma illa kisa.

Sarkin ya yi wannan furucin ne yayin taron tsaro na masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Katsina kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Online view pixel