An damke Likitan yan bindiga a jihar Katsina, ya bayyana dalilin da yasa yake musu aiki

An damke Likitan yan bindiga a jihar Katsina, ya bayyana dalilin da yasa yake musu aiki

  • Yan sanda sun damke mai kula da lafiyan tsagerun yan bindiga a Katsina
  • Matashin ya bayyana cewa shi ke sayar musu da maguna kuma yake musu jinya
  • Ya yi nadamar abinda yayi kuma idan aka yafe masa ba zai sake ba

Katsina - Wani ma'aikacin lafiya a jihar Katsina, Murtala Umar, ya bayyana yadda ya kasance mai kula da yan bindiga yayinda suka samu raunuka duk da cewa ya san yan ta'adda ne.

A ranar Litinin, hukumar yan sanda a jihar Katsina ta gabatar da shi gaban manema labarai a hedkwatar hukumar, rahoton Premium Times.

Malamin jinyan mai suna Murtala ya bayyanawa manema labarai cewa dole ce ta sa shi yake aiki da su.

Murtala na da shagon sayar da magunguna a Tashar Yar Alewa, dake karamar hukumar Danmusa.

Kara karanta wannan

Yadda jami'an tsaron UNIMAID suka afka dakunan kwanan dalibai mata, suka damke masu zanga-zanga

Al'ummar garin ne suka sanar da yan sanda yayinda suka zargi abinda yake yi.

Yace:

"Na yi karatu a Kwalejin kiwon lafiya da fasaha dake Kankia amma ban fara aiki ba. Yan bindigan na zuwa shagona don neman taimako kuma su biya ni."

Yace yana sane da cewa yan bindiga ne saboda suna zuwa da bindigoginsu, amma babu yadda ya iya da su.

Ya bayyana cewa "yayi nadamar abinda yayi kuma ba zai sake ba."

An damke Likitan yan bindiga a jihar Katsina, ya bayyana dalilin da yasa yake musu aiki
An damke Likitan yan bindiga a jihar Katsina, ya bayyana dalilin da yasa yake musu aiki Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

An damke wasu mata masu kaiwa yan bindiga man fetur a jihar Katsina

Hukumar yan sanda a jihar Katsina ranar Alhamis ta damke wasu mata uku da ake yiwa zargin kaiwa yan bindiga man fetur cikin daji a jihar.

Kakakin yan sandan jihar, SP Gambo Isah, a hira da manema labarai a Katsina, ya bayyana matan uku; Dija Umar, 50; Ummah Bello, 45; da Nusaiba Muhammad, 16 yan unguwar Malali, a cikin Katsina.

Kara karanta wannan

'Yan fashin daji sun koma hawa rakuma yayin da dokar siyan fetur a jarkoki ta tsananta

Kakin yan sandan yace an damke su ne a titin Katsina zuwa Jibiya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel