Da duminsa: Gwamnatin Kaduna ta tabbatar barkewar rikici a jihar, an kashe mutum 34

Da duminsa: Gwamnatin Kaduna ta tabbatar barkewar rikici a jihar, an kashe mutum 34

  • Gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa'i ya yi Alla-wadai da harin da aka kaiwa mutane Kaura
  • An tabbatar da mutuwar akalla mutum 34 kuma an kona gidaje
  • El-Rufa'i yayi alkawarin biyan kudin jinyan wadanda aka jikkata
  • An damke mutum biyu cikin wadanda ake zargi da aikata wannan abu

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar labarin kisan mutane talatin da hudu da yan bindiga sukayi a karamar hukumar Kaura ta jihar Kaduna ranar Lahadi.

Mun kawo muku cewa wasu batagari sun kona gidaje a kauyukan Madamai da Abun dake karamar hukumar Kaura a jihar Kaduna.

Kwamishanan tsaro da lamuran cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya saki jawabi ranar Litinin, 27 ga Satumba, 2021.

A cewarsa, kawo yanzu mutum 34 aka tabbatar da an kashe yayinda Sojoji suka kashe wutar daka cinnawa gidaje.

Kara karanta wannan

Dokar hana fita ta IPOB: Batagari sun bankawa motar kayan miya wuta a Enugu

Yace:

"Sojoji sun garzaya wajen kuma suma yan bindigan suka bude musu wuta, amma daga baya suka gudu da suka ji wutan annaru."

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Sun kona wasu gidaje a kauyen. Sojoji sun kashe wuta a gidaje uku, kuma sun ceto mutane shida."
"Kawo yanzu dai mutum 34 aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon harin. An garzaya da sauran da suka jigata asibiti a jihar Plateau."

Da duminsa: Tashin hankali yayinda rikici ya sake ballewa a Kaduna, mutum 30 sun hallaka
Da duminsa: Tashin hankali yayinda rikici ya sake ballewa a Kaduna, mutum 30 sun hallaka
Asali: Twitter

Gwamnan Kaduna ya yi alhinin abinda ya faru, yayi alkawarin biyan kudin jinyan wadanda ke asibiti

Samuel Aruwan ya bayyana cewa gwamna Nasir El-Rufa'i na jihar ya yi Alla-wadai da wannan abu.

Gwamnan ya ce gwamnatin jihar za ta dauki nauyin jinyar wadanda suka jikkata kuma suka jinya a asibiti yanzu.

Yace:

"Gwamnan El-Rufa'i ya bayyana cewa gwamnatin jihar zata dauki nauyin kudin jinyar wanda suka samu raunuka."

Kara karanta wannan

Kaduna: 'Yan bindiga sun kai farmaki coci, sun sheke mai bauta

Dan garin ya bayyana abinda ya gani

A cewar tsohon shugaban gamayyar matasan Kaura, Derek Christopher, yan bindigan sun dira garuruwan ne misalin karfe 5 na yammacin Lahadi suka bude musu wuta, rahoton Daily Trust.

A cewarsa:

"An garzaya da wasu asibiti don jinyarsu."

Legit tayi yunkurin tuntubar Kakakin hukumar yan sanda a jihar Kaduna, ASP Muhammad Jalige, amma bai daga wayarsa ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel