Da Ɗuminsa: Jam'iyyar PDP Ta Dakatar Da Jiga-Jiganta Biyu a Borno

Da Ɗuminsa: Jam'iyyar PDP Ta Dakatar Da Jiga-Jiganta Biyu a Borno

  • Babban jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party, PDP, ta dakatar da jiga-jiganta biyu a jihar Borno
  • 'Yan jam'iyyar da aka dakatar sun hada da tsohon dan takarar gwamna Mohammed Alkali Imam da tsohon shugaban PDP na jihar Zannah Gaddama Mustapha
  • An dakatar da su ne domin suna janyo rabuwar kan a jam'iyyar kamar yadda sakatare Yusuf Mohammed Dikko ya sanar

Jihar Borno - Rikicin cikin gida ya yi sanadin dakatar da manyan 'ya'yan jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party, PDP, biyu a jihar Borno, Daily Trust ta ruwaito.

Wadanda aka dakatar din sun hada da tsohon dan takarar gwamna Mohammed Alkali Imam da tsohon shugaban PDP na jihar Zannah Gaddama Mustapha.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar APC ta sake dage babban taron jam'iyya na jihohi zuwa wani lokaci

Da Ɗuminsa: Jam'iyyar PDP Ta Dakatar Da Jiga-Jiganta Biyu a Borno
Tambarin Jam'iyyar PDP. Hoto: Daily Trust
Asali: Facebook

Dalilin dakatar da jiga-jian na PDP?

Daily Trust ta ruwaito cewa Sakataren PDP na jihar Borno, Yusuf Mohammed Dikko, wanda ya sanar da dakatarwar yayin taron 'yan jarida a Maiduguri ya ce wadanda aka dakatar din suna raba kan 'yan jam'iyyar.

Ya ce jiga-jigan biyu duk sun ki amsa tambayoyin da aka yi musu dangane da korafin da shugabannin jam'iyyar na matakin mazabu da kananan hukumomi suka shigar a kansu.

Da aka tuntube shi domin ji ta bakinsa, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na Borno, Mustapha ya ce jam'iyyar bata kafa kwamitin ladabtarwa ba domin yin bincike a kan lamarin.

2023: Ba mu buƙatar Atiku ya sake takara, Ya tafi Dubai ya manta da mu tunda ya sha kaye a 2019, Ƙungiyar PDP

Kara karanta wannan

Jam’iyyar PDP ta kori tsohon gwamnan Neja Aliyu a matsayin memba na BoT, ta sanar da madadin shi

A wani labarin daban, wata kungiya mai suna People’s Democratic Party (PDP) Action 2023, ta bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kada ya sake takara a shekarar 2023 don ya yi watsi da jam'iyyar ya koma Dubai, UAE, tunda ya fadi zabe a 2019, rahoton Daily Trust.

Atiku, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben 2019, bai riga ya bayyana niyarsa na son sake takara ba a 2023, amma, dansa, Adamu Atiku Abubakar, ya tabbatar cewa zai sake takara.

Amma a martaninsa, Atikun ya ce ba watsi da jam'iyyar ta PDP ya yi ba, ya tafi yin karatun digiri na biyu ne a kasar waje.

Asali: Legit.ng

Online view pixel