Kungiyar Musulunci ta bayyana boyayyar hikimar jawo Fani-Kayode cikin Jam’iyyar APC
- Muslim Rights Concern ta yabi Cif Femi Fani-Kayode da ya dawo APC
- Kungiyar MURIC tace sauya-shekar ‘dan siyasar za ta amfani mutane
- Farfesa Ishaq Akintola yake cewa ‘dan siyasar ya yi koyi da mahaifinsa
Nigeria - Kungiyar Muslim Rights Concern (MURIC), tace mutanan Najeriya za su amfana da sauya-shekar da Femi Fani-Kayode ya yi zuwa jam’iyyar APC.
Shugaban kungiyar ta MURIC, Farfesa Ishaq Akintola ya fitar da jawabi a ranar Lahadi, yace ba za su shiga sahun sauran masu sukar sauya-shekan ‘dan siyasar ba.
Jaridar Vanguard ta rahoto Ishaq Akintola yana cewa akwai yiwuwar Femi Fani-Kayode ya sauka daga ra’ayoyin da yake a kai tun da ya shigo jam’iyya mai mulki.
“Fani-Kayode mutum ne wanda baro-baro yake goyon bayan masu kiran a barka kasa. Ana neman jawo yaki saboda aika-aikan wadanda yake mara wa baya.”
“A yau duk ta kare Fani-Kayode zai koma kiran a hada-kai a Najeriya a inda ya samu kansa.”
“A kan wannan ne muke yaba wa abin da mahaifin FFK, Remi Ade Fani Kayode ya yi a shekarun 1970s, ya ajiye siyasar kabilanci, ya hada-kai da Arewa.”

Source: UGC
MURIC take cewa Cif Remi Ade Fani Kayode ya yi hakan ne domin a samun hadin-kai a kasar.
A cewar kungiyar, a yau ‘dansa Femi Fani Kayode ya yi irin abin da tsohonsa ya yi a Najeriya. Yace ya kamata sauya-shekar da FFK ya yi ya fara daga zuciyarsa.
"Dole mu manta da cewa ya yi wa kowa kaca-kaca (har da shugaban MURIC) saboda sabanin fahimta, a yau sai a yaba masa na irin dattakun da ya nuna.”
A karshe Farfesa Ishaq Akintola ya yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya manta da abin da FFK ya yi masa a baya, ya karbe shi hannu biyu a APC.

Kara karanta wannan
‘Dan APC ya fito yana banbami, yace duk satar mutum, da ya shigo cikinsu ya zama Waliyyi
Obasanjo ya zama Jakadan zaman lafiya
Kwanakin baya aka ji labari cewa kungiyar AU ta ba Olusegun Obasanjo nauyin kawo zaman lafiya a Somaliya, Kenya, Sudan, da wasu kasashen Afrika ta gabas.
Olusegun Obasanjo ya fara karada kasashen domin kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Asali: Legit.ng
