Kungiyar Musulunci ta bayyana boyayyar hikimar jawo Fani-Kayode cikin Jam’iyyar APC

Kungiyar Musulunci ta bayyana boyayyar hikimar jawo Fani-Kayode cikin Jam’iyyar APC

  • Muslim Rights Concern ta yabi Cif Femi Fani-Kayode da ya dawo APC
  • Kungiyar MURIC tace sauya-shekar ‘dan siyasar za ta amfani mutane
  • Farfesa Ishaq Akintola yake cewa ‘dan siyasar ya yi koyi da mahaifinsa

Nigeria - Kungiyar Muslim Rights Concern (MURIC), tace mutanan Najeriya za su amfana da sauya-shekar da Femi Fani-Kayode ya yi zuwa jam’iyyar APC.

Shugaban kungiyar ta MURIC, Farfesa Ishaq Akintola ya fitar da jawabi a ranar Lahadi, yace ba za su shiga sahun sauran masu sukar sauya-shekan ‘dan siyasar ba.

Jaridar Vanguard ta rahoto Ishaq Akintola yana cewa akwai yiwuwar Femi Fani-Kayode ya sauka daga ra’ayoyin da yake a kai tun da ya shigo jam’iyya mai mulki.

“Fani-Kayode mutum ne wanda baro-baro yake goyon bayan masu kiran a barka kasa. Ana neman jawo yaki saboda aika-aikan wadanda yake mara wa baya.”

Kara karanta wannan

Femi Fani-Kayode: Sabon 'jagwal' ne ya shigo jam’iyyar APC, PDP

“A yau duk ta kare Fani-Kayode zai koma kiran a hada-kai a Najeriya a inda ya samu kansa.”
“A kan wannan ne muke yaba wa abin da mahaifin FFK, Remi Ade Fani Kayode ya yi a shekarun 1970s, ya ajiye siyasar kabilanci, ya hada-kai da Arewa.”
FFK da Isa Ali Pantami
Femi Fani Kayode da Isa Ali Pantami Hoto: www.bbc.com
Asali: UGC

MURIC take cewa Cif Remi Ade Fani Kayode ya yi hakan ne domin a samun hadin-kai a kasar.

A cewar kungiyar, a yau ‘dansa Femi Fani Kayode ya yi irin abin da tsohonsa ya yi a Najeriya. Yace ya kamata sauya-shekar da FFK ya yi ya fara daga zuciyarsa.

"Dole mu manta da cewa ya yi wa kowa kaca-kaca (har da shugaban MURIC) saboda sabanin fahimta, a yau sai a yaba masa na irin dattakun da ya nuna.”

Kara karanta wannan

‘Dan APC ya fito yana banbami, yace duk satar mutum, da ya shigo cikinsu ya zama Waliyyi

A karshe Farfesa Ishaq Akintola ya yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya manta da abin da FFK ya yi masa a baya, ya karbe shi hannu biyu a APC.

Obasanjo ya zama Jakadan zaman lafiya

Kwanakin baya aka ji labari cewa kungiyar AU ta ba Olusegun Obasanjo nauyin kawo zaman lafiya a Somaliya, Kenya, Sudan, da wasu kasashen Afrika ta gabas.

Olusegun Obasanjo ya fara karada kasashen domin kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Asali: Legit.ng

Online view pixel