Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi

Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi

  • Ambaliyar ruwa ta yi barna a rukunin gidajen Trademore a Lugbe babban birnin tarayya Abuja
  • Mazauna unguwar sun ce ambaliyar ruwar ya fara ne a ranar Litinin bayan ruwan sama mai karfi da aka yi
  • Kawo yanzu an gano gawarwakin mutane uku sannan ruwan ta lalata motocci da kayayyakin al'umma da dama

FCT, Abuja - A kalla gawarwakin mutane uku ne aka gano a safiyar ranar Litinin a rukunin gidaje na Trademore da ke Lugbe, babban birnin tarayya, Abuja, Premium Times ta ruwaito.

Rahoton na Premimum Times ya ce mazauna unguwar sun ce ambaliyar ruwan ya fara ne a safiyar ranar Litinin bayan ruwan sama da aka yi kamar da bakin kwarya.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun hallaka fasto a Kaduna, El-Rufai ya yi martani mai zafi

Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi
Barnar da ambaliyar ruwa ta yi a Trademore Estate, Abuja. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi
Hotunan barnar da ambaliyar ruwa ta yi a Trademore Estate, Abuja. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Ambaliyar ruwar ya yi sanadin bacin motocci da wasu kayayyakin mutane da dama a unguwar.

Jami'an hukumar kwana-kwana na birnin tarayya Abuja sun isa wurin a safiyar ranar Litinin domin kai wa mutane dauki.

Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi
Wata mota da ambaliyar ruwa ya bata a Trademore Estate. Abuja. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi
Hotunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

A kan samu irin wannan ambaliyar ruwar a unguwar a duk damina na kowanne shekara.

Ku saurari karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: