Gwamnatin Filato ta kara sassauta dokar hana fita a Jos ta Arewa, tare da dage dokar hana adaidaita sahu

Gwamnatin Filato ta kara sassauta dokar hana fita a Jos ta Arewa, tare da dage dokar hana adaidaita sahu

  • Gwamnatin Filato ta janye dokar hana tuka Keke NAPEP a garin Jos da kewaye tare da sassauta dokar hana zirga-zirga, a Karamar Hukumar Jos ta Arewa
  • Gwamnan Jihar, Simon Lalong, ne ya amince da hakan bayan kammala taron Majalisar Tsaron Jihar
  • A yanzu dokar hana zirga-zirga ta dawo daga karfe 10 na dare zuwa karfe 6 na safe

Filato - Gwamnatin jihar Filato ta sanar da sake sassauta dokar hana fita a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Dakta Makut Macham ya fitar, ya bayyana cewa gwamnati ta kuma dage haramcin da aka sanya a baya a kan tuka adaidaita sahu a jihar.

Gwamnatin Filato ta kara sassauta dokar hana fita a Jos ta Arewa, tare da dage dokar hana adaidaita sahu
Gwamnatin Filato ta kara sassauta dokar hana fita a Jos ta Arewa, tare da dage dokar hana adaidaita sahu Hoto: Punch
Asali: UGC

Macham ya bayyana cewa gwamnan ya amince da hakan ne a ranar Talata bayan taron kwamitin tsaro na jihar da aka gudanar a sabon gidan gwamnati a Jos, Aminiya ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kogi ga EFCC: Zargin waskar da kudi da ku ke yi daidai yake da labaran 'A sha ruwan tsuntsaye'

Sanarwar ta ce:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Daga ranar Laraba, 8 ga Satumba 2021, dokar hana fita a Jos ta Arewa za ta fara aiki daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.
“Wannan zai yi daidai da matsayin dokar hana fita a kananan hukumomin Jos ta Kudu da Bassa wanda har yanzu yana daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.
“Hakanan, Gwamna Lalong ya kuma amince da cewa daga ranar Laraba, 8 ga Satumba 2021, za a dage dokar hana zirga -zirgar adaidaita sahu daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma a kullum. Wannan yana nufin cewa ba za a bar wani adaidaita ya yi aiki tsakanin awanni 6 na yamma zuwa 6 na safe ba.”

Sai dai gwamnan, ya bayyana cewa haramcin babura a cikin garin Jos/Bukuru zai ci gaba da aiki, yana mai cewa za a ci gaba da tabbatar da ganin an kama masu laifin da kuma hukunta su kamar yadda doka ta tanada.

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: Gwamnatin Kaduna ta haramta safarar dabbobi daga wasu jihohi

Gwamnan ya yabawa al'umman jihar kan haɗin kai da fahimtar da suka nuna a lokacin hare-haren da kuma dokar hana fita.

Ya bukace su da su ci gaba da marawa gwamnati baya don dawo da zaman lafiya a fadin jihar, Channels TV ta ruwaito.

Kisan Jos: Na kudiri aniyar gurfanar da 'yan ta'adda a gaban kuliya, inji Buhari

A wani labarin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnatinsa ta kuduri aniyar cafke mutanen da ke da hannu a kashe-kashen da aka yi a jihar Filato.

A cikin watanni uku da suka gabata, hare-hare a sassa daban-daban na jihar sun yi sanadiyar mutuwar mutane sama da dari.

Buhari, wanda Boss Mustapha, sakataren gwamnatin tarayya (SGF) ya wakilta, a wani zaman tattaunawa tare da masu ruwa da tsaki a jihar a ranar Litinin 6 ga watan Satumba, ya bukaci tattaunawa mai dorewa don samar da zaman lafiya a Filato.

Kara karanta wannan

Kwanaki bayan ganawa da Tinubu, shahararren gwamnan APC ya magantu akan kudirin takarar shugaban kasa

Asali: Legit.ng

Online view pixel