Gwamnan PDP ya samu mukami mai muhimmanci daga Shugaba Buhari

Gwamnan PDP ya samu mukami mai muhimmanci daga Shugaba Buhari

  • Muhammadu Buhari ya nada gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin mamba a kwamitin kawo sauyi na fannin kiwon lafiya
  • Kwamitin da shugaban kasa ya kaddamar a ranar Litinin yana da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a matsayin shugabanta
  • Wasu fitattun likitocin kiwon lafiya kamar Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, suma membobin kwamitin ne

An nada Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin mamba a kwamitin kawo sauyi a fannin kiwon lafiya wanda mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ke jagoranta.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya kaddamar da kwamitin a ranar Litinin, 6 ga watan Satumba, jaridar The Cable ta ruwaito.

Gwamnan PDP ya samu mukami mai muhimmanci daga Shugaba Buhari
Gwamna Ifeanyi Okowa ya samu mukami mai muhimmanci daga Shugaba Buhari Hoto: Delta State Government
Asali: Facebook

A cewar wata sanarwa da daya daga cikin hadiman shugaba Buhari kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar, an kafa kwamitin ne don ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a bangaren.

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari ya ba Osinbajo shugabancin kwamitin da zai gyara kiwon lafiya a jihohi 36

Sauran membobin kwamitin sun hada da Osagie Ehanire, Ministan Lafiya da kuma Shugabannin Kungiyar Likitocin Najeriya (NMA), Kungiyar Magunguna ta Najeriya, kungiyar ma’aikatan jinya da kungiyar gwaje-gwaje ta Najeriya, Vanguard ta ruwaito.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Gidauniyar Bill & Melinda Gates da Vesta Healthcare Partners za su yi aiki a matsayin masu sa ido a cikin kwamitin.

Shugaba Buhari ya ba Osinbajo shugabancin kwamitin da zai gyara kiwon lafiya a jihohi 36

A baya mun kawo cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kafa kwamitin da zai fitar da tsare-tsare da dabarun gyara sha’anin kiwon lafiya a Najeriya.

Mai magana da yawun bakin shugaban Najeriyar, Malam Garba Shehu ya bayyana wannan a wani jawabi da ya fitar a ranar 6 ga watan Satumba, 2021.

Kamar yadda kuka samu labari a baya, mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ne zai jagoranci wannan kwamiti da zai yi wannan babban aiki.

Kara karanta wannan

Shugaban kasa ya yi sabon nadi, ya ba Osinbajo sabon aiki, ya nada shugaba a hukumar NCDC

Asali: Legit.ng

Online view pixel