Da Ɗumi-Ɗumi: Masu Garkuwa Sun Sace Mutane 18 a Wani Unguwa a Kaduna

Da Ɗumi-Ɗumi: Masu Garkuwa Sun Sace Mutane 18 a Wani Unguwa a Kaduna

  • Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kai hari wani unguwa a karamar hukumar Chikun na jihar Kaduna
  • Wasu mazauna unguwar sun ce maharan sun kai harin ne misalin karfe 12 na dare sannan sun sace mutum 18
  • A halin yanzu babu sanarwa daga rundunar yan sanda game da harin sai dai mazauna unguwar sun ce yan sanda sun isa wurin

Chikun, Jihar Kaduna - A ƙalla mutane 18 ne aka sace cikin adaidaita sahu (Keke Napep) a wani unguwa a ƙaramar hukumar Chikun na jihar Kaduna.

Daily Trust ta ruwaito cewa yan bindiga sun kai hari unguwar misalin ƙarfe 12 na dare.

Da Ɗumi-Ɗumi: Masu Garkuwa Sun Sace Mutane 18 a Wani Unguwa a Kaduna
Da Ɗumi-Ɗumi: Masu Garkuwa Sun Sace Mutane 18 a Wani Unguwa a Kaduna
Asali: Original

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun afka ofishin ƴan sandan Zamfara, sunyi kisa, sun sace bindigu AK-47 masu yawa

Shaidan gani da ido sun ce yan bindigan sun iso da yawa kuma bayan tada hankalin mutane a unguwar, suka yi awon gaba da mutane 18.

Wakilin Daily Trust ya ruwaito cewa har yanzu jami'an yan sanda suna unguwar.

Sai dai har yanzu ba a tabbatar da afkuwar lamarin daga wata majiya na hukuma ba.

Ku saurari ƙarin bayani ...

Asali: Legit.ng

Online view pixel