PDP ta samu abin yin magana, Ministan Buhari yace ana sata salin-alin a Gwamnatin APC

PDP ta samu abin yin magana, Ministan Buhari yace ana sata salin-alin a Gwamnatin APC

  • Jam’iyyar PDP ta maida martani a kan wasu kalamai da Rotimi Amaechi ya yi
  • Ministan yace watakila a samu wadanda ke sata a boye a Gwamnatinsu ta APC
  • PDP tace wannan ya tabbatar da abin da ta ke fada kan satar da ake ta tafkawa

Abuja - Jam’iyyar adawa ta PDP tace bayanan da aka ji Ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya na yi a kan gwamnatin APC, sun tabbatar da abin da ta ke fada.

Yadda Amaechi ya wanke PDP - Kola Ologbondiyan

PDP ta bakin Mai magana da yawunta, Kola Ologbondiyan ta ce abin da Ministan tarayyar ya fada, ya gaskata ikirarinta na cewa ana sata a gwamnatin nan.

A ranar Litinin, 30 ga watan Agusta, 2021, jaridar The Cable ta rahoto sakataren yada labaran na APC, Kola Ologbondiyan, ya na maida wa Ministan martani.

Kara karanta wannan

Wasu Shugabannin PDP na Neman Tada Rikici, Sun ce An Ware Su a Yakin Zaben Atiku

Jam’iyyar hamayyar tace kalaman Ministan sun tabbatar da barna da rashin gaskiyar da ake yi a karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

“Abin da Amaechi ya ambata ya nuna sata a boye yana cikin tarihin da APC za ta bari a mulki.”

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

“Wannan ya nuna abin da ya sa gwamnatin nan ta buge da furofaganda, ta gagara gurfanar da jami’anta da shugabannin APC da aka samu da rashin gaskiya.”

Buhari
Buhari a Aso Rock Hoto: www.premiumtimesng.com
Asali: UGC

PDP ta kalubalanci gwamnatin Buhari

Premium Times tace PDP ta kalubalanci shugaba Buhari ya yi bincike a kan jagororin APC da ake zargi da hannu a bacewar Naira tiriliyan 25 daga baitul-mali.

Jam’iyyar tace APC ta sace arzikin kasa, ta jefa ta a matsin tattalin arziki sau biyu a cikin shekaru shida, ta sa Najeriya ta zama hedikwatar talauci a Duniya.

Kara karanta wannan

APC ta Fallasa Abinda Ya Kawo Hargitsi A Gangamin PDP na Kaduna

PDP ta ce an sace Naira tiriliyan 9.3 a NNPC, bayan biliyoyin kudin makamai da NSA yace sun bace, da kudin da aka sata daga NHIS da NEMA a mulkin APC.

Ologbondiyan ya tabo zargin kudin da suka yi kafa a asusun hukumomin NPA, NIMASA, FMBN da FIRS da tsarin SIP, ya yi kira ga jama’a su guje wa APC a 2023.

Me Rotimi Amaechi ya fada?

Da aka yi hira da Amaechi kwanaki, yace babu mamaki akwai wasu da ke satar dukiyar gwamnati a boye, akasin abin da ya faru a lokacin mulkin PDP.

Ba kamar gwamnatin baya ba, wannan gwamnatin idan zaka saci kuɗi sai dai ka yi a sirrince. Ministan yace gwamnatinsu ta fi kowace gwamnati rike amana.

Asali: Legit.ng

Online view pixel