Ba zamu yarda ba: Kungiya tayi tsokaci kan karin farashin lantarki da gwamnati tayi

Ba zamu yarda ba: Kungiya tayi tsokaci kan karin farashin lantarki da gwamnati tayi

  • Wata kungiyar yakin samun ingancin wuta tayi Alla-wadai da kara farashin lantarki
  • Hukumar NERC ta bada umurnin kara farashin wuta daga gobe Laraba
  • Yan Najeriya da dama sun nuna rashin jin dadinsu kan wannan

Oyo - Gamayyar yakin samun inganci da saukin farashin wutan lantarki watau CARE, shiyyar jihar Oyo, ta yi Alla-wadai da karin farashin wuta da hukumar NERC tayi.

A jawabin da CARE ta saki ranar Talata a Ibadan, kungiyar ta yi watsi da wannan kari da hukumar NERC tayi, rahoton DN.

Tace:

"CARE tayi Allah-wadai da umurnin kara farashin wutan lantarki da hukumar NERC tayi."
"Kara farashin wuta a irin wannan lokaci da yan Najeriya ke fama da kuncin tattalin arziki sakamakon COVID-19 da kuma matsin tattalin arziki rashin tausayi ne."

Kara karanta wannan

Jami'an hukumar kwastam sun cafke wata mota dauke da bindiga da harsasai

"CARE na da ra'ayin cewa babu wani dalilin kara farashin wuta tunda karin da akayi a baya bai tsinana wani ingancin samun wuta ba."

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Maimakon haka, yawancin mutane na fama da karancin wutan lantarki sannan kuma ana tilastasu biyan kudi."

Ba zamu yarda ba: Kungiya tayi tsokaci kan karin farashin lantarki da gwamnati tayi
Ba zamu yarda ba: Kungiya tayi tsokaci kan karin farashin lantarki da gwamnati tayi Hoto: Discos
Asali: Facebook

Za'a kara kudin wutan lantarki ranar 1 ga Satumba

Kun ji cewa hukumar lura da wutar lantarkin Najeriya (NERC) ta umurci kamfanonin raba wutar lantarki 11 (Discos) su kara farashin wuta fari daga ranar 1 ga watan Satumba, 2021.

Bisa wani takarda da jaridar TheNation tayi ikirarin gani yau, hukumar NERC ta baiwa kamfanonin damar kara kudin ne a wasikar mai taken "Sanarwan Karin Farashi."

Hakazalika an tattaro cewa a wani takarda mai lamba ”023/EKEDP/GMCLR/0025/2021, kamfanin raba lantarkin Eko (EKEDC), ya sanar da kwastamominsa cewa za'a yi karin kudin wuta daga ranar 1 ga Satumba, 2021.

Kara karanta wannan

Babbar Magana: Ministan Buhari Ya Fallasa Yadda Ake Sata Ta Karkashin Kasa a Mulkin Shugaba Buhari

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng