Dakile matsalar tsaro: Jerin sabbin dokoki 10 da Masari ya kafa a jihar Katsina

Dakile matsalar tsaro: Jerin sabbin dokoki 10 da Masari ya kafa a jihar Katsina

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya kafa wasu sabbin dokoki goma domin shawo kan matsalar tsaron da ta addabi jihar sama da shekaru biyu yanzu.

A takardar da gwamnan da kansa ya rattafa hannu mai kwanar wata 30 ga Agusta, 2021 kuma Legit ta samu, gwamnan ya bada umurnin kulle wasu hanyoyi da kuma safarar wasu kayayyaki.

Hakazalika Gwamna Masari ya dawo da dokar hana yawo da babura da a daidaita sahu da dare.

Gwamnan yace wadannan dokoki zasu fara aiki ne daga ranar Talata, 31 ga watan Agusta.

Ga jerin dokokin busa sanarwar da gwamnatin jihar tayi:

1. Rufe hanyar Jibia-Gurbin har zuwa lokacin da hali yayi

2. Rufe titin Kankara-Sheme ga masu motocin haya

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Kotu ta tsare mutane 8 da ake zargi da yin garkuwa da matar kwamishinan Benue

3. Haramtawa manyan motoci daukan itace daga daji

4. An dakatad da sayar da dabbobi a kananan hukumomi 14 (Jibia, Batsari, Sfana, DanMusa, Kankara, Malumfashi, Charanci, Ma'adua, Kafur, Faskari, Sabuwa, Baure, Dutsinma, da Kaita.)

5. An haramta fitar da dabbobi daga jihar Katsina zuwa wata jiha a Najeriya

Dakile matsalar tsaro: Jerin sabbin dokoki 10 da Masari ya kafa a jihar Katsina
Dakile matsalar tsaro: Jerin sabbin dokoki 10 da Masari ya kafa a jihar Katsina
Asali: Facebook

6. An haramta daukar mutum 3 kan babur kuma sama da mutum uku kan Keke Napep

7. An haramta sayar da baburan da ba sabbi ba a kasuwar Charanci

8. An dawo da dokar hana amfani da babura da Keke Napep daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe

9. An haramta sayarwa masu jarkuna man fetur a gidajen mai

10. Gidajen Mai biyu kacal aka amince su sayar da mai na fiye da N5000 a kananan hukumomi 14 (Jibia, Batsari, Sfana, DanMusa, Kankara, Malumfashi, Charanci, Ma'adua, Kafur, Faskari, Sabuwa, Baure, Dutsinma, da Kaita.)

Wannan ra'ayin ka ne: FG ta yi wa Masari martani kan cewa mutane su kare kansu daga ƴan bindiga

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya koka, masu rike da madafan iko sun haramta masa ganin Shugaba Buhari

A bangare guda, gwamnatin tarayya ta yi watsi da kiran da Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina da takwararsa na Jihar Benue, Samuel Ortom, da wasu kungiyoyi da mutane suka yi na cewa mutane su kare kansu daga 'yan bindiga.

Ministan Harkokin 'Yan sanda, Mohammed Dingyadi, yayin jawabin shekara-shekara na ma'aikatarsa karo na biyu a hedkwatar yan sanda a Abuja ya ce gwamnati bata goyon bayan mutane su dauki makamai da kansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng