Kungiyar kare hakkin jama'a ta kai karar Buhari a kotu kan ‘bacewar’ Naira Biliyan 106 a 2018

Kungiyar kare hakkin jama'a ta kai karar Buhari a kotu kan ‘bacewar’ Naira Biliyan 106 a 2018

  • SERAP ta na karar gwamnatin Najeriya a babban kotun tarayya da ke Abuja
  • Kungiyar ta bukaci a binciki wasu kudi da ake zargin sun bace daga ma’aikatu
  • Za ayi shari’a da Shugaba Muhammadu Buhari, AGF da Ministar kudi a kotu

Abuja - Kungiyar nan ta 'Socio-Economic Rights and Accountability Project' wanda aka fi sani da SERAP, ta shigar da kara a kan gwamnatin Najeriya.

Socio-Economic Rights and Accountability Project ta kuma zuwa kotu

Legit.ng ta ji cewa wannan kungiya mai cin gashin kan-ta, ta maka gwamnatin Muhammadu Buhari a gaban wani babban kotun tarayya da ke Abuja.

SERAP ta bayyana wannan ne a shafinta na Facebook a ranar Asabar, 22 ga watan Agusta, 2021.

Kungiyar na zargin shugaba Muhammadu Buhari da kin hukunta wadanda suke da laifi a zargin bace war Naira biliyan 196 daga ma’aikatun gwamnati.

Kara karanta wannan

Hukumar leken asiri ta tura sako ga lauyan Zakzaky kan batun hanashi fita waje

Kamar yadda muka ji, sauran wadanda za su amsa laifi a kotu sun hada da Ministan shari’a, kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami SAN.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Haka zalika ana karar Ministar tattalin arziki da tsare-tsaren kasafin kudi na kasa, Zainab Ahmed.

Buhari
Shugaban Najeriya Buhari Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Wannan kungiya ta shigar da kara a kotu ne bayan zargin da ofishin mai binciken kudi na kasa ya yi na cewa N105,662,350,077.46 sun bace a shekarar 2018.

Ana zargin kudin sun yi batar-dabo ne daga ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya wadanda aka fi sani da MDAs 149 shekaru uku da suka wuce.

Me SERAP ta ke nema a kotu?

“A kara mai lamba FHC/ABJ/CS/903/2021 da aka shigar a kotun tarayya da ke Abuja a makon jiya, ana neman a tursasa wa shugaba Buhari ya binciki zargin bacewar N106bn.”
“(Buhari) ya tabbatar an hukunta duk wanda aka samu da laifi, kuma a dawo da kudin da aka dauka.”

Kara karanta wannan

FIRS na neman hanyoyin tatsar kudi, Twitter da sauran kamfanoni za su soma biyan haraji a 2022

“Dawo da wannan kudi zai taimaka wajen ganin gwamnatin tarayya ta rage adadin bashin da ta ke ci domin ta cike gibin da aka samu a kasafin kudin tattalin arziki.”

Kawo yanzu ba a sa ranar da Alkali zai fara sauraron wannan kara a babban kotun tarayyar ba.

Samuel Ortom ya na shirin zuwa kotu

Gwamna Samuel Ortom ya gargadi Gwamnatin Tarayya a kan yunkurin farfado da hanyoyin kiwon dabbobi, yace hakan ya ci karo da tsarin mulkin da ake kai a yau.

Samuel Ortom ya ce ba zai yiwu a wannan zamani, a dauki fili a ba dabbobi domin su yi kiwo ba. Tuni gwamnan ya ankarar da lauyoyinsa cewa su fara shirin tafiya kotu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel