Duk da an kafa dokar hana fita, miyagu sun yi mamaya, an sake hallaka mutane a Jihar Filato
- ‘Yan kabilar Irigwe sun ce an kai masu hare-hare, an hallaka mutane biyar a Bassa
- Shugaban kungiyar mutanen Irigwe yace an kashe masu mutane cikin lokacin kulle
- Wasu Bayin Allah sun bace bayan harin da aka kai a kauyukan Dong da Tafi-Gana
Jos - ‘Yan bindiga sun kuma kai wani danyen hari a karamar hukumar Bassa, Filato, a lokacin da gwamnati ta bada umarnin kowa ya zauna a gida.
An auka wa mutanen Dong, Tafi-Gana
Jaridar This Day ta fitar da rahoto a ranar Alhamis, 19 ga watan Agusta, 2021, ta ce an hallaka mutane akalla biyar a sabon hare-haren da aka kai.
An kai harin ne a lokacin da ba a gama makokin wasu matafiya da aka kashe a hanyar Jos ba.
Wadanda suka yi wannan ta’adi sun auka wa kauyen Tafi-Gana cikin dare a ranar Talata, 17 ga watan Agusta, 2021, a lokacin da mutane suke barci.
Haka zalika ‘yan bindiga sun kai hari a kauyen Dong, a nan ma an hallaka mutum daya kamar yadda wani dattijo, Danjuma Auta, ya fada wa ‘yan jarida.
Da yake magana a ranar Laraba, shugaban kungiyar Irigwe Development Association, Mista Ezekiel Bini, ya tabbatar da aukuwar wannan lamarin.

Asali: UGC
Ezekiel Bini yace an kashe mutum biyar, kuma an nemi mutane hudu an rasa inda suka shiga bayan ta’adin.
“Gaskiya ne an kashe mutane biyar a danyen harin da aka kawo mana. Yanzu haka za mu je mu gana da gwamna kan kashe-kashen da ake yi a Bassa.”
Su wanene su ka yi wannan aika-aika?
Rahoton yace ana zargin makiyaya ne suka yi wannan danyen aiki a garin Bassa, sai dai kuma babu wata hujja da za ta iya gaskata zargin da ake yi.

Kara karanta wannan
Kisan Filato: Duk wanda ke gaggawar karbar belin wanda ake zargi za a kwamushe shi, Lalong
Shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, watau MACBAN, tace babu hannunta a sabon harin da aka kai.
Da take maida martani, Kungiyar Miyetti Allah ta kasa, tace bai kamata a rika alakanta kowane mummunan hari irin wannan da Fulani a Filato ba.
Kisan matafiya kusan 40
Bayan an hallaka fasinjoji da-dama a hanyar Jos, Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya bukaci gwamnati ta hukunta wadanda ke da hannu a laifin.
"Za mu dauki dukkan matakai da shari’a ta yadda da su. Muna kira ga musulmai, muna bada hakuri cewa ka da mu dauki wani mataki a hannunmu.”
Asali: Legit.ng