Jerin ka'idoji 3 da gwamnatin Buhari ta ba Twitter kafin a dage dokar haramtata

Jerin ka'idoji 3 da gwamnatin Buhari ta ba Twitter kafin a dage dokar haramtata

  • Gwamnatin Buhari ta amince Twitter ya dawo aiki a Najeriya, sannan an ba kamfanin ka'idoji
  • Kamfanin ya amince da bukatar gwamnati, ya kuma sanar da cewa zai kafa ofishi a Najeriya
  • Najeriya ta lissafo wasu ka'idoji guda 3 da ta ce dole kamfanin ya cika su kafin ya dawo aiki

Bayan dakatar da Twitter a Najeriya, kamfanin da gwamnatin Najeriya sun cimma matsaya.

A cewar Ministan Yada Labarai da Al'adu, Lai Mohammed, wanda ya sabunta bayani ga 'yan Najeriya kan batun, ya ce kamfanin ya amince zai biya wasu bukatun gwamnati, in ji PR News.

Jerin ka'idojin da gwamnatin Buhari ta ba Twitter kafin a dage dokar haramtata
Ministan Yada Labarai, Lai Mohammed | Hoto: dailytrust.com
Asali: Depositphotos

Ya ce Twitter ya amince da yin wadannan:

1. Samar da ofishi a Najeriya tare da yin rijista da hukumar harkokin kasuwanci

Ya ce saboda son yin kasuwanci a Najeriya, dole ne su kasance suna da ofishi a cikin kasar. Ya ce saboda haka dole ne su samar da adireshi, The Cable ta kara da cewa.

Kara karanta wannan

Twitter ta yi martani bayan gwamnati ta sanar da dage dokar haramtata a Najeriya

2. Samar da wakilin Twitter a Najeriya

Mohammed ya kuma ce ya zama dole kamfanin ya dauki wakilan kasar da zai zama wakilin Twittera Najeriya. Ya ce dole ne wakilin ya kasance ma’aikacin Twitter wanda zai iya zama mai sadarwa tsakanin Najeriya da Twitter.

"Mun yi imanin cewa yana da mahimmanci Twitter ya kasance yana da wakilin kamfani wanda ke sama. Domin ya iya kai korafi kai tsaye daga Najeriya zuwa Twitter."

3. Yin rijista da hukumomin da abin ya shafa

Mun kuma umarci Twitter, baya ga yin rijistar kamfanin a Najeriya, dole ne kuma ya yi rajista da hukumomin da suka dace kamar su NIPDA, NCC da hukumar watsa labarai.

Twitter ta yi martani bayan gwamnati ta sanar da dage dokar haramtata a Najeriya

Kara karanta wannan

Tsohon minista ya fadi abinda zai hana mutanen kudu maso gabas shugabanci a 2023

A wani labarin, Gwamnatin tarayya, ta hanyar ministan yada labarai da al'adu, Lai Mohammed ta sanar da dage dokar hana Twitter, kana kamfanin zai bude ofishinsa a Najeriya.

Mohammed ya bayyana haka ne a ranar Laraba, 11 ga watan Agusta, yayin da yake zantawa da wakilan gidan gwamnati bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya a Abuja.

Ministan ya ce ya zuwa yanzu, gwamnati ta dage dakatar da shafin tare da wasu sharudda wadanda wasu daga ciki sun hada da yin rijista da Hukumar Harkokin Kasuwanci (CAC).

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.