Matar tsohon shugaban kasa, Hadiza Shagari ta mutu bayan fama da cutar korona

Matar tsohon shugaban kasa, Hadiza Shagari ta mutu bayan fama da cutar korona

  • Matar marigayi tsohon Shugaban kasa, Hadiza Shehu Shagari ta amsa kiran Allah
  • Hajiya Hadiza ta rasu a yau Alhamis, 12 ga watan Agusta bayan ta yi fama da cutar korona
  • Za a yi jana'izarta bayan sallar La'asar a babban masaLlacin kasa da ke Abuja

Allah ya yi wa Hadiza Shagari, matar marigayi tsohon Shugaban kasa Shehu Shagari rasuwa, tana da shekaru 80 a duniya, jaridar Daily Nigerian ta ruwaito.

Wata sanarwa da ‘dan tsohon shugaban kasar, Bala Shagari ya fitar, ya bayyana cewa ta mutu ne sakamakon cutar korona a cibiyar killace masu cutar da ke Gwagwalada.

Uwargidar tsohon shugaban kasa, Hadiza Shagari ta mutu tana da shekaru 80
Hadiza Shagari ta rasu ne sakamakon cutar korona a cibiyar killace masu cutar da ke Gwagwalada Hoto: Daily nigerian
Asali: UGC

Ya kuma bayyana cewa za a yi jana’izarta a yau Alhamis, 12 ga watan Agusta, bayan sallar la’asar a babban masallacin kasa da ke Abuja, Solacebase ta ruwaito.

Sanarwar ta zo kamar haka:

“Mun rasa ta da sanyin safiyar yau, 12 ga watan Agusta 2021, da misalin karfe 3:00am, bayan ta yi fama da Covid-19 a Cibiyar Killace masu ita na Gwagwalada da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Dawowar Korona karo na 3: Gwamnatin tarayya ta yi magana kan sake kafa dokar kulle

“Hajiya Hadiza Shehu Shagari ta na da shekaru 80 a duniya. Za a yi Sallar Jana'izarta a yau, da karfe 4:00 na yamma bayan sallar la’asar, a Masallacin Kasa, Abuja.”

A wani labarin kuma, gwamnatin tarayya ta ce bata shirya kafa wani sabon dokar kulle ba duk da dawowar cutar COVID-19 a fadin tarayya.

Channels TV ta ruwaito cewa ministan lafiya, Dr Osagie Ehanire, ya bayyana hakan ne ranar Alhamis, 12 ga Agusta, a taron mako-mako na hira da manema labarai a fadar shugaban kasa, Abuja.

Legit.ng ta tattaro cewa Ministan yace adadin mutanen da suka kamu bai kai a kakaba sabuwar dokar kulle ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng