Shahararren fasto ya yi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce

Shahararren fasto ya yi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce

  • A kokarin kara dankon zumunci tsakanin addinai, Reverend Father Peter Ayanbadejo ya yi bikin Eid-el-Kabir tare da Musulmai a wani babban masallacin jihar Ogun
  • An wallafa hotunan malamin addinin kiristan da takwarorinsa na musulmai a shafukan sada zumunta kuma abun ya burge 'yan Najeriya
  • A tuna cewa daukacin al’umman musulmai a kasar sun yi bikin Eid-el-Kabir wanda aka fi sani da babban Sallah a ranar Talata, 20 ga Yuli

Babban fasto, Reverend Father Peter Ayanbadejo ya sa mutane tofa albarkacin bakunansu a shafukan sada zumunta bayan ya yi bikin Eid-el-Kabir tare da Musulmai a wani babban masallaci a karamar hukumar Ogun Waterside da ke jihar Ogun.

Shafin Facebook na The Partner Newspaper, Ijebu-Ode-Ode Diocese ne ya wallafa hotunan malamin na addinin kirista tare da takwarorinsa Musulmai.

Shahararren fasto yayi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce
Faston ya je masallaci domin taya Musulmi bikin babban Sallah Hoto: The Partner Newspaper, Ijebu-Ode Diocese
Asali: Facebook

Reverend Father Ayanbadejo ya kasance shugaban Ogbere Catholic Deanery.

A wasu daga cikin hotunan, ana iya ganin faston zaune a kan tabarma a cikin masallacin. Hakanan za'a iya ganin sa yana ɗaukar hoto tare da wasu al’umman musulmai.

Kara karanta wannan

Alkali ya bada dama EFCC ta karbe kudi da kadarorin na-kusa da tsohuwar Minista, Diezani

Lamarin ya burge mutane da dama

Johnpaul Orebanjo ya ce:

"Jagora mai kyau Allah ya karbi aikinka amin ta wurin shugabanmu Yesu."

Godwin Sunday Alphonsus ya yi sharhi:

"Kyakkyawan jagora wannan ita ce hanya daya da za a sanar da su cewa Allah daya ne kuma mu 'ya'yansa ne."

Ademiloye Odunayo Mary ta rubuta:

"Mun gode shugaba."

A wani labari na daban, mun ji cewa Masarautar Daura ta nada wa dan Shugaban kasa Muhammadu Buhari, Yusuf, sarautar Talban Daura.

Babban mai ba Shugaban kasa shawara a kafofin watsa labarai, Mallam Garba Shehu ne ya sanar da labarin nadin da aka yiwa Yusuf a yau Talata, 20 ga watan Yuli a wani wallafa da yayi a shafinsa na Facebook.

An nada masa sarautar ne tare da Musa Daura, wanda yanzu shine Dan Madamin Daura.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng