Shahararren fasto ya yi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce

Shahararren fasto ya yi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce

  • A kokarin kara dankon zumunci tsakanin addinai, Reverend Father Peter Ayanbadejo ya yi bikin Eid-el-Kabir tare da Musulmai a wani babban masallacin jihar Ogun
  • An wallafa hotunan malamin addinin kiristan da takwarorinsa na musulmai a shafukan sada zumunta kuma abun ya burge 'yan Najeriya
  • A tuna cewa daukacin al’umman musulmai a kasar sun yi bikin Eid-el-Kabir wanda aka fi sani da babban Sallah a ranar Talata, 20 ga Yuli

Babban fasto, Reverend Father Peter Ayanbadejo ya sa mutane tofa albarkacin bakunansu a shafukan sada zumunta bayan ya yi bikin Eid-el-Kabir tare da Musulmai a wani babban masallaci a karamar hukumar Ogun Waterside da ke jihar Ogun.

Shafin Facebook na The Partner Newspaper, Ijebu-Ode-Ode Diocese ne ya wallafa hotunan malamin na addinin kirista tare da takwarorinsa Musulmai.

Shahararren fasto yayi bikin Sallah tare da Musulmai a Masallaci, kyawawan hotuna sun janyo cece-kuce
Faston ya je masallaci domin taya Musulmi bikin babban Sallah Hoto: The Partner Newspaper, Ijebu-Ode Diocese
Asali: Facebook

Reverend Father Ayanbadejo ya kasance shugaban Ogbere Catholic Deanery.

A wasu daga cikin hotunan, ana iya ganin faston zaune a kan tabarma a cikin masallacin. Hakanan za'a iya ganin sa yana ɗaukar hoto tare da wasu al’umman musulmai.

Kara karanta wannan

Alkali ya bada dama EFCC ta karbe kudi da kadarorin na-kusa da tsohuwar Minista, Diezani

Lamarin ya burge mutane da dama

Johnpaul Orebanjo ya ce:

"Jagora mai kyau Allah ya karbi aikinka amin ta wurin shugabanmu Yesu."

Godwin Sunday Alphonsus ya yi sharhi:

"Kyakkyawan jagora wannan ita ce hanya daya da za a sanar da su cewa Allah daya ne kuma mu 'ya'yansa ne."

Ademiloye Odunayo Mary ta rubuta:

"Mun gode shugaba."

A wani labari na daban, mun ji cewa Masarautar Daura ta nada wa dan Shugaban kasa Muhammadu Buhari, Yusuf, sarautar Talban Daura.

Babban mai ba Shugaban kasa shawara a kafofin watsa labarai, Mallam Garba Shehu ne ya sanar da labarin nadin da aka yiwa Yusuf a yau Talata, 20 ga watan Yuli a wani wallafa da yayi a shafinsa na Facebook.

An nada masa sarautar ne tare da Musa Daura, wanda yanzu shine Dan Madamin Daura.

Asali: Legit.ng

Online view pixel