Kungiyoyin Arewa 75 sun sa miliyan 100 ga duk wanda ya iya kamo Shugaban IPOB, Kanu

Kungiyoyin Arewa 75 sun sa miliyan 100 ga duk wanda ya iya kamo Shugaban IPOB, Kanu

  • Northern Consensus Movement ta na shelar a cafko mata Nnamdi Kanu
  • Duk wanda ya kawo Nnamdi Kanu cikin koshin lafiya, zai samu N100m
  • Kungiyoyin Arewan suna so a cigaba da shari’a da shugaban IPOB a kotu

Gamayyar kungiyoyin Arewa a karkashin Northern Consensus Movement sun bada sanarwar kyautar kudi ga wanda zai iya cafko mata Mazi Nnamdi Kanu.

A ranar Alhamis, kungiyar Northern Consensus Movement ta ce za ta bada Naira miliyan 100 a matsayin tukuici ga duk wanda ya kawo shugaban kungiyar IPOB.

Jaridar The Nation take cewa wadannan kungiyoyi na Arewa su na so a dawo da Nnamdi Kanu gida ne domin ya cigaba da fuskantar shari’ar da ake yi da shi.

KU KARANTA: Matasan Arewa sun yi magana a kan yunkurin kashe Shugaban EFCC

Kungiyoyin sun bayyana haka da suke zanta wa da ‘yan jarida a Abuja, su ka zargi Kanu da dakarun ESN da kitsa harin da aka kai wa ‘Yan Arewa a Kudu.

Dr. Awwal Aliyu ya yi magana a madadin Northern Consensus Movement, ya na rokon Amurka, Ingila da kasashen Turai su izo keyar Kanu, ayi masa hukunci.

Vanguard ta rahoto Dr. Awwal Aliyu ya na jawabi:

“Kungiyar Northern Consensus Movement, gamayyar kungiyoyin Arewa masu zaman kansu fiye da 75 sun daukarwa kansu, a matsayinsu na ‘yan kasa cewa:

KU KARANTA: Kotu ta bada belin Mai shekara 52 da ‘danta, da ake zargi da laifi

Mazi Nnmadi Kanu
Shugaban IPOB, Nnmadi Kanu Hoto: saharareporters.com
Asali: UGC

Laifuffukan Shugaban IPOB, Nnmadi Kanu

“Ana neman Nnamdi Kanu da laifin laifuffuka, da haddasa kashe-kashen da aka yi wa mutanen Arewa a yankin Kudu maso gabas ta hanyar kalaman kiyayyarsa.”
“Muna so ya amsa laifuffukansa na kisan rayuka da barnata dukiyar mutanen Arewa da su ke zaune a Kudu maso yammacin Najeriya, suna kasuwancinsu na halal.”
“Saboda haka mun sa kyautar kudi na N100m a matsayin rabon wanda zai iya kawo mana da shi da ransa, cikin koshin lafiya, ba tare da an yi masa rauni ba.” inji Aliyu.

Kungiyar ta na so a kawo mata wannan mutum, ta kai shi wurin jami’an tsaro, su cigaba da shari’a da shi, ya amsa laifuffukansa na cin amanar kasa da ta’addanci.

A jiya ne aka ji cewa wasu 'yan bindiga sun sace dalibai a jihar Kebbi. Wadannan miyagu sun yi amfani da motar mahaifin wata daliba wajen sace daliban makarantar.

Daga baya wani 'Dan majalisar wakilai a majalisar tarayya ya gaskata faruwar wannan lamari.

Asali: Legit.ng

Online view pixel