Nan da shekara 2, sai yan Najeriya sun jinjinawa shugaba Buhari: Fadar Shugaban kasa

Nan da shekara 2, sai yan Najeriya sun jinjinawa shugaba Buhari: Fadar Shugaban kasa

- Shugaba Buhari ya cika shekaru shida kan kujerar mulkin Najeriya

- Hadimansa sun lissafa nasarorin da ya samu a wannan shekarun

- Yan Najeriya sun ce rashin tsaro ya karu a cikin wadannan shekaru shidan

Fadar shugaban kasa, a ranar Juma'a, ta bayyana cewa kafin karewar wa'adin shugaba Muhammadu Buhari a 2023, ko masu adawa sai sun jinjinawa masa.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, ya bayyana hakan a jawabin murnar cikar Buhari shekaru 6 kan mulki.

Adesina ya lissafa jerin nasarori da ayyukan da shugaba Muhammadu Buhari yayi.

Hadimin ya bayyana cewa gwamnatin maigidansa ta samu dimbin nasarori a bangaren Tattalin arziki, tsaro, samar da aikin yi, jin dadin al'umma, dss.

A cewarsa "wadanda basu bari siyasa ko adawa ya hana su ganin gaskiya ba zasu tabbatar da cewa an yi aiki."

DUBA NAN: An damke hadimin gwamna Sule, yan sanda 2, Kansila da wasu 14 kan satan karafunan layin dogo

Nan da shekara 2, har yan adawa sai sun jinjinawa shugaba Buhari: Fadar Shugaban kasa
Nan da shekara 2, har yan adawa sai sun jinjinawa shugaba Buhari: Fadar Shugaban kasa Hoto: @channelstv
Asali: Twitter

DUBA NAN: Nan da watan Yuli zamu fara ginin layin dogon Kaduna zuwa Kano, Minista Amaechi

Adesina ya ce "Daga ayyukan jin dadi, zuwa harkar kudi, ilimi, wasanni, yaki da rashawa, gine-ginen gidaje, man fetur, harkokin waje, da sauran su, gwamnatin nan ta samu nasarori kuma ya kamata Najeriya suyi alfahari."

"Ga masu cewa: "Ba ma ganin komai da sukeyi. Ba ma samun labarin komai, nan da shekara biyu da ikon Allah, zasu jinjinawa shugaban kasa, har yan adawa mafi tsanani."

A bangare guda, mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, a ranar Laraba, ya ce yan Najeriya su daina yaudarar kansu cewa abubuwa na tafiya daidai a Najeriya.

Sultan Saad ya bayyana hakan ne a taron tattauna matsalar tsaro dake gudana a Abuja, rahoton Channels.

"Kada mu yaudari kanmu cewa abubuwa na tafiya daidai, abubuwa sun tabarbare. Mun san hakan, kuma muna gani," Sultan yace.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng