Da duminsa: An alanta 'dan Idris Deby, Mahamat Kaka, matsayin mukaddashin shugaban kasar Chadi

Da duminsa: An alanta 'dan Idris Deby, Mahamat Kaka, matsayin mukaddashin shugaban kasar Chadi

- Majalisar Sojin kasar Chadi ta alanta mukaddashin shugaban kasar

- Wannan ya biyo bayan sanar da kisan shugaban kasar, Idris Deby, ranar Talata

- Mahamat na daya daga cikin 'yayan marigayin kuma babban jami'in sojan kasar

Bayan mutuwar mahaifinsa filin daga, hukumar Sojin kasar Chadi ta alanta nadin 'dan marigayi, Mahamat Kaka, a matsayin mukaddashin shugaban kasar.

Kakakin hukumar Sojin Chadi ya sanar.

Mahamat Idriss Deby Itno, Janar ne mai tauraro 4 a hukumar Sojin kasar kuma ya nada shekaru 37 da haihuwa.

A cewar Aljazeera, Mahamat Deby zai jagoranci kasar nan na tsawon watanni 18 yayinda majalisar Soji ke shirin gudanar da zabe.

Da duminsa: An alanta 'dan Idris Deby, Mahamat Kaka, matsayin mukaddashin shugaban kasar Chadi
Da duminsa: An alanta 'dan Idris Deby, Mahamat Kaka, matsayin mukaddashin shugaban kasar Chadi PHOTO: MARCO LONGARI / AFP
Asali: Twitter

KU KARANTA: Milyan 17 muka biya don a sake mana 'yayanmu 39 amma 10 aka saki, Iyayen daliban Kaduna

Mun kawo muku rahoton cewa shugaban kasar Chadi, Idris Deby, ya riga mu gidan gaskiya, bayan samun nasara a zaben kasar.

Rahotanni sun nuna cewa Idris Deby ya mutu ne sakamakon harbin da akayi masa a faggen yaki da yan tawaye.

An saki sakamakon nasararsa a zaben ne ranar Litnin.

Idris Deby ya mutu yana mai shekaru 68.

Ya hau mulkin kasar bayan tawaye a shekarar 1990. Ya lashe kashi 79.3% na zaben da aka gudanar ranar 11 ga Afrilu.

Ya kwashe shekaru 30 yana mulki.

DUBA NAN: Ba za'a kara farashin man fetur ba a watan Mayu, Shugaban NNPC

Asali: Legit.ng

Online view pixel