Tsawon mako guda kenan Korona ba ta yi kisa ba a Najeriya

Tsawon mako guda kenan Korona ba ta yi kisa ba a Najeriya

- Da alamu cutar Korona ta fara yin bankwana tare da shirin barin Najeriya a yankin Afrika

- Kasar ta samu raguwar adadin masu kamuwa da kwayar cutar, hakanan ma masu mutuwa

- Kasar ta shaida mako gudu da kwayar cutar ta Korona ba ta kashe ko da mutum daya ba

Alkalumman da hukumar dakile cututtuka masu yaduwa a Najeriya (NCDC) ke fitarwa game da cutar korona a kasar ya nuna cewa tsawon mako daya kenan cutar ba ta yi kisa ba a fadin kasar, BBC ta rahoto.

Alkalumman wadanda cutar ta kashe ba su sauya ba tun daga ranar 31 ga watan Maris zuwa 7 ga watan Afrilu inda cutar ta kashe jimillar mutum 2,058 tun shigowarta

KU KARATA: Yawaitar hatsarin mota yasa Dangote ya kaddamar da cibiyar horar da direobi

Tsawon mako guda kenan Korona ba ta yi kisa ba a Najeriya
Tsawon mako guda kenan Korona ba ta yi kisa ba a Najeriya Hoto: usnews.com
Asali: UGC

Alkalumman da hukumar ta fitar ranar Talata sun nuna cewa karin mutum 58 da sun kamu da cutar korona a Najeriya.

Jihar Legas da cutar da ta fi kamari ce ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar a kasar da mutum 32.

KU KARANTA: Rikicin addini a Gombe: Gwamna Yahaya ya tallafawa wadanda rikici ya rutsa dasu

A wani labarin, Gwamnatin Indiya ta bayar da gudummawar allurai 100,000 na rigakafin Korona ga Najeriya, Daily Trust ta ruwaito.

An yi jigilar magunguna 100,000 na allurar rigakafin Covishield, wanda aka kirkira a kwalejin Serum ta Indiya, zuwa Hukumar Kula da Kiwon Lafiyar Kiwon Lafiyar Firamare ta Kasa (NPHCDA), a cewar wata sanarwa daga Babban Hukumar ta Indiya a Abuja.

Sanarwar ta ambato Babban Kwamishinan Indiya a Najeriya, Abhay Thakur, yana cewa samar da alluran rigakafin ga Najeriya ya dace da kudurin Firayim Minista Narendra Modi, wanda aka yi a UNGA a watan Satumbar 2020, cewa:

Asali: Legit.ng

Online view pixel