Fani Kayode ya musanta cin zarafin ma'aikatansa na cikin gidansa, ya garzaya gaban kotu

Fani Kayode ya musanta cin zarafin ma'aikatansa na cikin gidansa, ya garzaya gaban kotu

- Rikicin Femi Fani Kayode da tsohuwar matarsa, Precious Chikwendu, ya cigaba da yawo a kafafen sada zumunta

- A makon da ya gabata ne wani bidiyon mai raino a gidansa wanda yake bayyana tsananin zalincinsa da muguntarsa yayi ta yawo

- Saidai ɗan siyasar ya ce sam ba gaskiya bane bidiyon, an shirya shi ne musamman don a ɓata masa sunansa kuma ba zai yarda ba

Tun bayan rikicin tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani Kayode da tsohuwar matarsa, Precious Chikwendu, ya fallasa a idon duniya, bayan mutuwar aurensu ake ta daga akan wanda zai riƙe yaransu guda hudu, tsakanin shi da matarsa.

A ranar Juma'ar data gabata, 19 ga watan Maris aka sake ganin wani bidiyon ministan da yayi ta yawo a kafafen sada zumunta wanda yake nuna tsananin muguntarsa.

Bidiyon da ya janyo cece-kuce iri-iri a kafafen sada zumunta kamar yadda aka ga Fani-Kayode riƙe da guduma yana tsoratar da wani ma'aikacinsa na gida akan ya yi masa laifi kamar zai buga masa gudumar.

KU KARANTA: Hoton matashin bature sanye da kayan NYSC ya janyo cece-kuce

Fani Kayode ya musanta cin zarafin tsohuwar ma'aikaciyarsa, ya garzaya gaban kotu
Fani Kayode ya musanta cin zarafin tsohuwar ma'aikaciyarsa, ya garzaya gaban kotu. Hoto daga Femi Fani-Kayode, Jubril Oladimeji Olaiya
Asali: UGC

KU KARANTA: Onnoghen: Buhari ya fattakeni ne bayan an ce masa na gana da Atiku a Dubai

Fani-Kayode ya musanta zargin da ake masa na cutar da makusantansa kuma ya lashi takobin maka duk wanda yake da hannu a yada wannan mummunan labari akansa zuwa kotu.

A wani labari na daban, Dino Melaye, tsohon sanatan da ya wakilci jihar Kogi ta yamma, yace babbar damfarar da ta taba faruwa a Afrika shine yadda aka goyawa Buhari baya ya samu shugabancin kasa a 2015.

Melaye ya sanar da hakan ne a ranar Juma'a yayin da ya bayyana a wani shiri na gidan talabijin na Channels.

Jaridar The Cable ta ruwaito cewa, Melaye, wanda yanzu dan babbar jam'iyyar adawa ce ta PDP, ya bar jam'iyyar APC a shekarar 2018.

Aisha Khalid ma'aikaciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018.

Ta kwashe shekaru biyu tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu.

Za a iya bibiyar Aisha a shafinta na Twitter @DiyarKatsinawa

Asali: Legit.ng

Online view pixel