Da dumi-dumi: Gwamnan jihar Oyo ya bada umarnin sake bude kasuwar Sasha a yau

Da dumi-dumi: Gwamnan jihar Oyo ya bada umarnin sake bude kasuwar Sasha a yau

Yanzu-yanzun nan Gwamnan Makinde na jihar Oyo ya sake buɗe kasuwar Sasha bayan rufe ta na tsawon kwanaki biyo bayan rikicin kabilanci tsakanin Hausawa da Yarbawa a cikin kasuwar.

Mun ruwaito muku irin asarar da aka tafka a yayin rikicin tare da rayukan da rikicin ya hallaka.

Don samun zaman lafiya ya dawo cikin al’ummar Shasha, biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin Yarbawa da Hausawa a kasuwar, Gwamna Seyi Makinde, a safiyar ranar Talata, ya ba da umarnin sake bude kasuwar ba tare da bata lokaci ba.

An sami umarnin sake bude kasuwar ne a yayin ganawa da shugabannin Al’ummar Shasa, wanda aka gudanar a dakin taro na Western Hall a Sakatariya dake Ibadan.

Karin bayani nan kusa...

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng