Yanzu-yanzu: Ƴan Boko Haram sun ƙona gidaje fiye da 140 a ƙauyukan Borno, sun sace dabobi da kayan abinci

Yanzu-yanzu: Ƴan Boko Haram sun ƙona gidaje fiye da 140 a ƙauyukan Borno, sun sace dabobi da kayan abinci

- Yan bindiga sun kai hari a wasu kauyuka uku a karamar hukumar Biu da ke kudancin jihar Borno

- Garuruwan da yan ta'addan suka kai wa harin sun hada da Egiri, Zira I da Zira II inda suka kone gidaje, suka sace kaya

- Majiyoyi sun ce wannan shine karo na biyu da yan ta'addan ke kai hari a kauyen da ke karamar hukumar Biu

Wasu da ake zargi mayakan kungiyar ta'addanci ta Boko Haram sun kai hari wasu kauyuka a karamar hukumar Biu jihar Borno inda suka kone gidaje a kalla guda 140.

Bayan kone gidajen yan ta'addan sun kuma sace kayayyakin abinci da dabobi kamar yadda TVC News ta ruwaito.

Yanzu-yanzu: Ƴan Boko Haram sun ƙona gidaje fiye da 140 a kauyukan Borno
Yanzu-yanzu: Ƴan Boko Haram sun ƙona gidaje fiye da 140 a kauyukan Borno. Hoto: @thecableng
Asali: Twitter

Kauyukan da abin ya shafa sun hada da Egiri, Zira I da Zira II.

Zira na da nisan kilomita 5 daga kauyen Gur da aka kai hari a ranar Juma'a da ta gabata inda mutum hudu suka riga mu gidan gaskiya sannan aka kone gidaje da ababen hawa.

KU KARANTA: An fara bincikar jami'in Hisbah da aka kama da matar aure a ɗakin Otel a Kano

Zira da Gur garuruwa ne da ke kusa da Buratai, garin su tsohon babban hafsan sojojin kasan Nigeria, Janar Yusuf Tukur Buratai.

A cewar majiyoyi, wannan shine karo na biyu da yan ta'addan ke kai hari kauyen a cikin wata guda.

Wata majiya daga karamar hukumar Biu ta tabbatar wa TVC News barnar da yan ta'ddan suka yi a garuruwan guda uku.

DUBA WANNAN: 'Yan bindiga sun tsere bayan arangama da sojoji a Katsina

A wani labarin, kun ji cewa Sanata Iyiola Omisore, tsohon mataimakin gwamnan jihar Osun, daga karshe ya koma jam'iyyar All Progressives Congress (APC).

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa Omisore, a ranar Litinin, 15 ga watan Fabarairu ya ziyarci mazabarsa ta 6, Moore, a Ile-Ife, a tare da tawagar mataimakin gwamna, Benedict Alabi, domin ya karbi katinsa na APC.

Omisore ya yi takarar kujerar gwamna a shekarar 2018 a karkashin inuwar jam'iyyar Social Democratic Party (SDP).

Aminu Ibrahim ɗan jarida ne kuma ɗalibi mai neman ilimi. Ya yi karatun digiri na farko a Jami'ar Ahmadu Bello Zaria, yanzu yana karatun digiri na biyu a Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Ya shafe tsawon shekaru 5 yana aikin jarida inda ya samu gogewa a ɓangaren rubutun Hausa akan fanoni da suka shafi siyasa, mulki, wasanni, nishadi, da sauransu.

Aminu Ibrahim ne ya samu lambar yabo na zakaran editan shekarar 2020.

Za'a iya bibiyarsa a shafinsa na Twitter a @ameeynu

Asali: Legit.ng

Online view pixel