Kyakyawar budurwa lauya ta ce ta gaji da zama babu miji, tana bukatar wanda za su ci dukiyarta tare (Hotuna)

Kyakyawar budurwa lauya ta ce ta gaji da zama babu miji, tana bukatar wanda za su ci dukiyarta tare (Hotuna)

- Wata kyakkyawar lauya mai suna Barrkhadija, ta yi wata wallafa a Twitter wacce ta janyo cece-kuce

- A cewarta, duk da ta samu daukaka mai tarin yawa amma rayuwa bata mata dadi tunda bata da miji

- Kamar yadda lauyar tace, tana bukatar namijin da za ta dinga kashe dukiyarta tare da shi

Wata kyakkyawar lauya mai daukaka tayi wata wallafa a shafinta na kafar sada zumuntar zamani ta Twitter wacce ta janyo cece-kuce.

Budurwar mai suna Barrister Khadijah Umar, mai amfani da suna @Barrkhadijah, ta ce rayuwa babu miji bata da dadi, komai nasarar da mace ta samu a rayuwa.

Wannan wallafar ta ta ci karo da ta wasu mata wadanda suke nuna cewa macen da take samun fiye da N500,000 duk wata, bata bukatar namiji a rayuwarta.

Kyakkyawar lauyar ta nuna cewa kudi ba matsalarta bace, namiji ne kadai matsalarta. Kamar yadda ta wallafa, "Ina bukatar namijin da zamu dinga cin kudina tare da shi.

KU KARANTA: Hotunan ziyarar da Zulum ya kai wa mafarautan da Boko Haram suka kaiwa hari

Kyakyawar budurwa lauya ta ce ta gaji da zama babu miji, tana bukatar wanda za su ci dukiyarta tare
Kyakyawar budurwa lauya ta ce ta gaji da zama babu miji, tana bukatar wanda za su ci dukiyarta tare. Hoto daga @BarrKhadijah
Asali: Twitter

Wannan wallafar ta janyo cece-kuce iri-iri inda wani abba_dra cewa yayi: "Eh! Kuma duk wani namiji mai hankali, dukiya, ilimi, nasara da daukaka, akwai wata mace wacce ta tsaya masa. Dole mutum ya dogara da wani."

Mubaraksaba1 ya ce: "Haka rayuwa take 'yar uwa, yau da gobe sai Allah. Allah ya taimakemu."

Wata UmeorizuP ta ce: "Mu din dai muke korafin cewa bamu bukatar namiji, yanzu kuma mun samu daukaka muna bukatar namiji. Toh, ga dai mu nan."

KU KARANTA: Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa Iyan Zazzau, Alhaji Bashir Aminu rasuwa

A wani labari na daban, Gwamnatin tarayya ta gurfanar da Omoyele Sowore da wasu mutane hudu a gaban wata kotun majistare da ke Wuse Zone 2, Abuja, jaridar Leadership ta wallafa.

Rundunar 'yan sandan Najeriya ce ta gurfanar da Sowore a kan jagorantar zanga-zangar da suka yi wa gwamnati a ranar 31 ga watan Disamban 2020 a Abuja.

An gurfanar da shi tare da wasu mutane hudu a kan zarginsu da ake da lafifuka uku, lamarin da suka musanta aikatawa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel