'Yan bindiga sun koma Sabuwa cikin fushi bayan guduwar mutanen da suka sace, sun sake sace wasu 9

'Yan bindiga sun koma Sabuwa cikin fushi bayan guduwar mutanen da suka sace, sun sake sace wasu 9

- Yan bindiga sun sake kai hari garin Albasun Liman Sharehu da ke karamar hukumar Sabuwa a Jihar Katsina

- A hrin da suka kai na biyu, yan bindigan sun sake yin awon gaba da mutane guda tara don maye gurbin 8 da suka tsere

- Mutanen da aka yi garkuwar da su sun samu nasarar tserewa ne a yayin da 'yan bindigan da suka sace su ke sharbar barci

Wasu 'yan bindiga, cikin fushi, sun sake kai hari garin Albasun Liman Sharehu dake yankin karamar hukumar Sabuwa a Jihar Katsina tare da yin garkuwa da mutane tara.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ‘yan bindigar sun sake kai harin kauyen ne da sanyin safiyar ranar Laraba.

'Yan bindiga sun koma Sabuwa cikin fushi bayan guduwar mutanen da suka sace, sun sake sace wasu 9
'Yan bindiga sun koma Sabuwa cikin fushi bayan guduwar mutanen da suka sace, sun sake sace wasu 9. Hoto: @Channelstv
Asali: UGC

Wakilin Daily Trust ya ruwaito cewa daga cikin mutanen da 'yan bindigar suka yi garkuwar da su akwai wani dalibin aji biyar a babbar sakandire ta Damari, wanda aka sace tare da mahaifinsa.

DUBA WANNAN: An yanke wa ƴan ta'adda 168 hukuncin ɗaurin rai-da-rai - Rahoto

Kafin wannan harin, 'yan bindiga sun kai hari kauyen a ranar Kirsimeti tare da yin garkuwa da mutane takwas cikinsu har da matan aure biyu.

Sai dai, dukkan mutanen takwas da aka sace tare da yin garkuwa da su a makon da ya gabata sun samu damar tserewa yayin da ‘yan bindigar ke bacci.

A cewar wata majiya da ke kauyen, ‘yan bindigar sun fusata ne shine suka sake dawowa sakamakon tserewar mutanen tare da kama wasu a matsayin madadinsu.

KU KARANTA: Kotu ta tura wani gidan yari saboda yi wa Gwamna Badaru ƙazafi a Facebook

A kwanakin baya ne Farfesa Zulum ya ce duk da kisan manoma 43 da mayakan kungiyar Boko Haram su ka yi a Zabarmari, tsaro ya karu a jihar a karkashin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Farfesa Zulum, ya bayyana hakan ne ranar Lahadi yayin da ya karbi bakuncin kungiyar dattijan arewa a karkashin jagorancin shugabanta, Ambasada Shehu Malami, da kuma sakatarenta, Audu Ogbeh.

Hakan na kunshe ne a cikin jawabin da gwamnatin jihar Borno ta fitar ranar Litinin mai taken 'Zulum: Duk da kashe-kashe, shaidu a kasa sun nuna cewa an fi samun zaman lafiya a karkashin mulkin Buhari a Borno.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel